ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Dakatar Da Karuwar Hare-hare A Kan Likitoci – Ra’ayinmu

by Sulaiman
4 years ago
likitoci

A halin yanzu ya zama dole asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya su bada sanarwar gargadi ga marasa lafiya da iyalansu ta cewa likitoci da ma’aikatan lafiya na da hakkin gudanar da ayyukansu ba tare da tsoron barazana ko tsoron kai hare-hare a kan su ba a yayin da suke gudanar da ayyukansu na ceto rayuwar al’umma. Tabarbarewar lamarin hare-hare a kan likitoci da jami’an lafiya a kasar nan ya kai ga haka musamman ganin yadda ake fuskantar karancin likitoci kasar nan, inda wasu kasashen duniya ke yi wa likitocinmu tayin kudade masu tsoka tare da yanayin aiki mai dadin gaske.

Sai kuma ga su wadanda suka zabi zama a cikin gida don aikin su na ceto rayuwar al’umma suna fuskantar hare-hare daga marasa lafiya da iyalansu. A ‘yan wattanin nan an samu karuwar hare-haren a kan likitoci daga marasa lafiya da iyalansu da basu gamsu da wani abu da likitocin suka gudanar ba yayin jinyar ‘yanuwan nasu ko kuma suna zargin sakacin Likitocin ne suka yi sanadiyyar rasuwar ‘yanuwan nasu. Daga dukkan alamu hukumomin asibitocin da jami’an tsaro da hukumomin garuruwan da asibitocin suke basu da karfin da za su iya kawo karshen wannan lamarin da yake karuwa a kullum.

Rahoton hari na baya-bayan nan ya faru ne ana ‘yan kwanaki a shiga sabuwar shekarar nan a asibitin koyarwa na Jami’ar Ilorin da ke Jihar Kwara inda wasu iyalan mara lafiya daya mutu suka farmaki daya daga cikin likitocin asibitin abin da ya sa hukumar asibitin ta kwace gawar dan’uwan mutanen. Dalilin da mutane suka bayar na kai ma Likitan harin shi ne wai sakacinsa ne ya kai ga rasuwar danuwan nasu.

ADVERTISEMENT

Hukumar asibitin ta nemi a tabbatar da hukunta mutanen da suka aikata wannan laifin yayin da kuniyar Likitocin asibitin suka yi yajin aiki na kwana biyar, amma daga dukkan alamu hare-haren na cigaba da aukuwa babu wata alama ta yiwuwar dakatar da shi.

A bayaninsa, shugaban kungiyar likitoci na Jihar Kwara, Dakta Ola Ahmed, ya ce, a halin yanzu ire-iren wannan hari yana faruwa a kusan duk mako a sassan jihar abin da kuma yake zama tashin hankali ga likitoci da sauran ma’aikatan lafiya. A wani rahoto irin wannan lamarin ya faru a watan Fabrairu na shekarar 2022 a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Akure ta Jihar Ondo, danuwan wani mara lafiya ne ya yi wa wani Likita dukan kawo wuka.

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

A wani lamarin kuma, Shugaban Kungiyar Likitoci reshen Jihar Bauchi, Dakta Adamu Sambo a taron manema labarai da aka yi a watan Yuli na shekarar 2022, ya bayyana yadda aka kai wa wani Likita hari, inda yake cewa, “A ranar 8 ga watan Yuli na shekarar 2022, Dakta Mohammed Sani, wanda babban jami’in asibitin ne a Babban Asibitin garin Misau, a yayin gudanar da aikinsa wani danuwan mara lafiya ya kai masa hari da gatari da nufin kashe shi, ba zamu amince da wannan haukar a aikin mu na ceto rayuwar al’umma ba.”

“Koma menene koken mutane, ya kamata su mika koken ne ga hukumar da ta dace maimakon daukar doka a hannunsu. Wannan mutumin ya shigo ba tare da sanin halin da ake ciki ba ya kama wani likitan ma da baya cikin wadanda suka yi jinyar danuwan nasa ya shiga saransa da gatari har sau hudu.”

Haka kuma a watan Agusta na shekarar data gabata, iyalan wata mara lafiya sun kai wa wani likiitan mata hari inda suka ji masa mummunan ciwo a kansa, kungiyar likitoci na yankin Abuja sun nuna damuwarsu a kan hare-hare a kan likitoci da dukkan ma’aikatan lafiya a yankin dama kasar gaba daya.”
Kungiyar ta bayyana damuwarta musamman a kan sabbin likitoci dama wadanda suka tsufa in aka lura da yadda aka cusa lamarin hare-haren a asibitocinmu a ‘yan shekarun nan.
Wadannan hare-haren kamar yadda suke faruwa a Nijeriya yana nuna irin halin takaicin da al’umma ke ciki ne a Nijeriya a kan haka yakamata a nemo kwararru a bangaren kula da mutane masu fushi don a wannan lokacin kusan duk wanda ka taba zaka ga yana cikin fushi ne.

Tabbas ana fuskantar talauci, ga kuma tashin hankalin da harkokin ‘yanta’adda masu garkuwa da mutane suka dorawa al’umma da kuma halin tashin hankali da jami’an tsaronmu ke jefa mutane a ciki, lamarin yana matukar shafar tunanin al’umma, daga ka taba mutum sai kawai ya fashe maka. Bayan tabbatar da ganin an hukunta masu kai wa likitoci hari ya kamata hukumomin asibitocinmu su samar da yanayin bayar da shawarwari da magungunan warkar da damuwa ba wai kawai ga marasa lafiya ba har ma da iyalansu da masu jinyar marasa lafiyar gaba daya, musamman ganin wasu ‘yanuwan basu iya fuskantar labarin mutuwar ‘yanuwansu, su kuma kyautata mu’amalarsu da iyalan marasa lafiya.

A matsayinmu na gidan jarida muna sane da sakaci da rashin iya aiki na wasu likitoci da ma’aikatan lafiya wanda hakan ya kan kai ga rasa rayuwar marasa lafiyar da suke jinya. Kamar kowanne lokaci kuma ba a kai ga hukunta su, a kan haka muke kira ga mahukuntan asibitoci su samar da kafar da iyalan marasa lafiya za su iya kai koke a kan likitoci da ma’aikatan lafiya a cikin gaggawa a kuma tabbatar da an yi cikakken bincike tare da hukunta wanda aka a samu da laifi, wannan zai matukar taimaka wa tare da kwantar da hankalin iyalan marasa lafiya, rashin wannan ne yake haifar da daukar doka a hannun su.

likitoci
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe
  • Sulaiman
    GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara
  • Sulaiman
    Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026
  • Sulaiman
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

MASU ALAKA

Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Next Post
Matsalar Tsaro Na Ci Gaba Da Fatattakar Al’umma Bayan Cikar Wa’adin Disamba

Matsalar Tsaro Na Ci Gaba Da Fatattakar Al’umma Bayan Cikar Wa’adin Disamba

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.