ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukukuwan Maulidi: Ministan Abuja Ya Taya Mazauna Birnin Murna

by Sulaiman
3 years ago
Ministan Abuja

Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Barista Nyesome Wike, ya taya daukacin mazauna babban birnin tarayya murnar bikin Mauludi, inda ya bukace su da su bi tsarin zaman lafiya, tausayi da hadin kai a tsakaninsu.

A sakonsa na bikin Mauludi ga mazauna garin, Ministan ya bukaci al’ummar Musulmi da sauran mazauna babban birnin tarayya Abuja da su hada kai, su yi amfani da bikin a matsayin wata dama da za su sake jaddada aniyarsu ta juriya, soyayya da kyautatawa kamar yadda Annabi Muhammad (SAW) ya koyar.

  • Bukukuwan Maulid: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Laraba Ranar Hutu
  • Gwamnatin Tarayya Zata Gina Manyan Tituna Na Zamani A Abuja-Lagos Da Fatakwal-Lagos

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Ministan ya sanya wa hannu da kansa, wadda aka raba wa manema labarai a Abuja a ranar Talata, inda ta ce: “Abin farin ciki ne in mika gaisuwata ta musamman a madadin hukumar babban birnin tarayya Abuja ga daukacin mazauna Babban Birnin Kasar (FCT) akan taya murna da farin ciki ga zagayowar wannan gagarumin biki na Mauludi. Wannan rana mai muhimmanci ita ce ranar da aka haifi fiyayyen halitta Annabi Muhammad (SAW) kuma lokaci ne da muke bukatar koyarwarsa ta aminci da tausayi da hadin kai.

ADVERTISEMENT

“Mauludi ba wai murnar bikin maulidin ne kawai ba; wata dama ce a gare mu da ya dace mu taru a matsayinmu na mazauna babban birnin tarayya Abuja domin tabbatar da aniyarmu ta bin dabi’un hakuri da kauna da kyautatawa kamar irin yadda Annabi Muhammad SAW ya yi ta wa’azantarwa ba tare da gajiya ba. Lokaci ne da ya kamata mu tuna da mahimmancin tausayawa da kyawawan halaye na hadin kai wadanda ya kamata su jagoranci mu’amalar mu da juna.

“Allah ya sa wannan bikin Mauludin ya kawo mana zaman lafiya da walwala da budi. Mu tuna da darussan da Annabi Muhammad ya wa’azantar da mu, mu yi kokarin koyi da kyawawan dabi’unsa a cikin rayuwarmu ta yau da kullum”. Inji ministan

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

Ministan abuja
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

MASU ALAKA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
Manyan Labarai

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Next Post
Gwamna Yusuf

Duk Da Hukuncin Kotu, Gwamna Yusuf Ya Amince Da Kashe Naira Biliyan 3 Kan Ayyuka

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.