Sojojin rundunar haɗin gwiwa ta Arewa maso Yamma (JTF), ‘Operation FANSAN YAMMA’, sun ceto mutane 12 a wasu daban-daban da suka gudanar a ƙananan hukumomin Kaura Namoda da Tsafe na Jihar Zamfara.
A Kaura Namoda, sojojin sun mayar da martani ga kiran neman ɗauki bayan ’yan ta’adda sun kutsa cikin wani gida a yankin Tsohon Tasha.
Bayan musayar wuta da ’yan ta’addan, sojojin sun tilasta musu tserewa ta wani kogi, inda suka bar mutane shida da suka yi garkuwa da su.
Bayan ceto su, an kwashe mutanen zuwa wurin tsaro sannan aka sake haɗa su da iyalansu, kamar yadda Jami’in Yaɗa Labarai na JTF Arewa maso Yamma, Laftanar Kanar Aliyu Danja, ya bayyana.
A wani samame na daban a ƙaramar hukumar Tsafe, sojojin da ke sintiri a kan babbar hanya sun yi karo da ’yan ta’adda suna ƙoƙarin tare wata motar Sharon a ƙauyen Kwanoni.
Sojojin sun garzaya wurin tare da musayar wuta da ’yan ta’addan, lamarin da ya tilasta musu dakatar da harin tare da guduwa zuwa cikin dajin da ke kusa.
Jami’in ya ce wannan matakin ya kuma taimaka wajen ceto mutane shida, tare da hana ’yan ta’addan aiwatar da shirin satar mutanen.
Rundunar ta ce ayyukan na daga cikin ƙoƙarin da take yi na tarwatsa ayyukan ’yan ta’adda da kuma kare rayukan mutane a Jihar Zamfara.














