ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
33 minutes ago
PDP

Jam’iyyar adawa ta PDP a jihar Bauchi ta yi watsi da rahotannin da ke cewa tsarin jam’iyyar a jihar ya rushe ya koma cikin jam’iyyar Allied Peoples Movement (APM), inda ta bayyana iƙirarin a matsayin ƙarya da kuma aikin wasu masu sojar-gona.

Mai ba jam’iyyar shawara kan harƙoƙin shari’a, Barista Yahaya Garkuwa, ne ya bayyana hakan a ranar Talata yayin wani taron manema labarai da ya gudana a sakatariyar PDP da ke samun goyon bayan Ministan Abuja, Nyesom Wike, da ke kan titin Maiduguri Bypass, Bauchi.

Garkuwa ya ce jam’iyyar PDP da doka ta amince da ita a Jihar Bauchi ita ce wadda Hon. Ibrahim Kassim Toro ke jagoranta, yayin da a matakin ƙasa jam’iyyar ke ƙarƙashin jagorancin Hon. Abdulrahman Mohammed.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana cewa an daɗe ana kai rikicin shugabancin jam’iyyar gaban kotuna, inda kotuna daban-daban suka tabbatar da tsarin shugabancin da jam’iyyar ta amince da Abdulrahman.

A cewarsa, babbar kotun tarayya ta taɓa tabbatar da kwamitin riƙon kwarya da Abdulrahman Mohammed ke jagoranta a matsayin sahihin shugabancin PDP a matakin ƙasa.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Ya ce daga bisani ɓangaren Tanimu Turaki ta ɗaukaka ƙara kan hukuncin, amma kotun ɗaukaka ƙarar ta tabbatar da hukuncin, tare da amincewa da shugabancin Abdulrahman Mohammed a matakin ƙasa da kuma shugabancin Ibrahim Kassim Toro a Jihar Bauchi.

Garkuwa ya ƙara da cewa daga ƙarshe an kai batun gaban Kotun Ƙoli bayan ɓangaren adawa ya nuna rashin gamsuwa da hukuncin kotun daukaka kara.

Ya yi iƙirarin cewa hukuncin Kotun Ƙoli ya ƙara tabbatar da matsayinsu, inda ya ce ɓangaren Tanimu Turaki ba shi da goyon bayan doka.

Mai ba jam’iyyar shawara kan harkokin shari’ar ya zargi ɓangaren da ke adawa da su da komawa yin sojan-gonar shugabannin jam’iyyar da kuma yaɗa labaran ƙarya game da PDP bayan sun kare dukkan hanyoyin shari’ar da suke da su.

Ya ce, “Yanzu da hukuncin Kotun Ƙoli ya rufe musu duk wata hanya, sun fara sojan-gonar cewa su ne shugabannin PDP. Sun yanke shawarar haifar da ruɗani ta hanyar gaya wa jama’a cewa tsarin PDP ya rushe ya koma APM.”

Garkuwa ya jaddada cewa sahihan mambobin PDP suna nan cikin jam’iyyar kuma ba su fice zuwa wata jam’iyyar siyasa ba. “Mu, sahihan mambobin PDP, muna nan cikin PDP. Ba mu shiga wata jam’iyyar siyasa ba; har yanzu muna cikin PDP.”

Ya kuma bayyana cewa shugabancin PDP na Bauchi na shirin ɗaukar matakin shari’a kan wasu mutane da ake zargin suna bayyana kansu a matsayin jami’an jam’iyyar ba tare da izini ba.

Garkuwa ya yi kira ga jama’a da su yi watsi da jita-jitar cewa PDP ta haɗe da wata jam’iyya, yana mai jaddada cewa PDP ita ce jam’iyyar da doka ta amince da ita a jihar.

Ya kuma ƙalubalanci ɓangaren da ke adawa da su da ya bayyana sunayen ‘yan takarar da ya ce sun tsayar domin shiga zaɓen shekarar 2027.

Ya ce, “Idan da gaske su mambobin PDP ne, su bayyana sunayen ‘yan takararsu. Ba su da ‘yan takara.”

Garkuwa ya tabbatar wa magoya bayan jam’iyyar cewa PDP tana nan daram kuma a shirye take ta shiga babban zaben shekarar 2027. “PDP ba ta rushe zuwa wata jam’iyyar siyasa ba. PDP tana nan daram, PDP tana da ƙarfi kuma tana cikin shiri tsaf domin babban zaben shekarar 2027.”

Mai ba jam’iyyar shawara kan harkokin shari’ar ya samu rakiyar shugaban jam’iyyar na jiha, da sauran jami’an jam’iyyar, masu ruwa da tsaki da kuma magoya baya a wajen taron manema labaran.

Ya jaddada cewa PDP ta tsayar da ‘yan takara masu nagarta waɗanda za su iya samun nasara a zaben, inda ya tuna cewa jam’iyyar ce ta aiwatar da wasu daga cikin muhimman ayyukan ci gaba a Jihar Bauchi da kuma faɗin ƙasar nan a lokacin da take mulki.

Ya bayyana cewa Peoples Democratic Party (PDP) ta tsayar da Hon. Usman Adamu Ahmed Suphi a matsayin ɗan takararta na gwamna a Jihar Bauchi a babban zaben shekarar 2027, yayin da Alhaji Abdulkadir Aliyu Bababa zai kasance mataimakinsa.

PDP
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
PDP
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.