Wata da ake zargi da kasancewa mamba a ƙungiyar safarar yara, Adejoke Popoola, ta amsa cewa ta sayar da wasu daga cikin ’ya’yanta biyu da ta haifa, tare da satar wasu yara 19 domin sayar da su.
Popoola ta bayyana hakan ne yayin da take magana da manema labarai a hedikwatar Rundunar ’Yansandan Jihar Oyo da ke Ibadan, inda ta ce ta shiga harkar tun watan Oktoban 2024.
Wadda ake zargin ta ce ta sayar da jariri namiji da kuma tagwaye, inda ta bayyana cewa wani asibiti da ke Ogeere ne ya siya kuma biya ta N300,000 kan tagwayen.
Ta ce idan mutumin da ya yi mata cikin ya ƙi ɗaukar nauyin cikin, sai ta sayar da jaririn, inda a wasu lokuta ake biyanta tsakanin N80,000 zuwa N120,000 kan kowane yaro.
Popoola ta kuma ce tana da ’ya’ya bakwai, wasu daga cikinsu sun yi aure, yayin da ƙaramin ɗanta ke da shekara shida, babban kuma yana da shekara 34.
A cewarta, wata mata da ta yi aiki tare da ita a kasuwar Ogeere ce ta koya mata yadda ake satar yara.
Ta kuma yi ikirarin cewa daga cikin yara 19 da ake zarginta da sacewa, shida sun mutu, yayin da 13 ke raye.













