‘Yan bindiga sun kai hare-hare a wasu al’ummomi na ƙaramar hukumar Giwa a Jihar Kaduna, inda suka kashe mutane biyu, suka jikkata mutum ɗaya tare da yin garkuwa da wasu 26.
Jami’in Hulɗa da Jama’a na ‘Kaduna Vigilance Service (KadVS)’, Yunusa Shehu, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Talata.
Ya ce hare-haren sun faru ne a ƙauyukan Tunburku, Tudun Amada da Kallon Kura da ke ƙaramar hukumar.
A cewar Shehu, ’yan bindigar sun kai hare-haren ne kusan lokaci guda a Tunburku da ke gundumar Kidandan da Tudun Amada da ke gundumar Kadage, a safiyar ranar Litinin.
Ya ce an kashe Alhaji Surajo da Alhaji Ado a Tunburku, yayin da aka yi garkuwa da mutane 26 a Tudun Amada.
Ya ƙara da cewa wani mazaunin yankin, Ayyuba Usman, ya samu raunuka sakamakon harin da ya faru da misalin ƙarfe 12:30 na dare.
Jami’in ya kuma ce ’yan bindigar sun yi awon gaba da shanun wasu mazauna yankin a wasu hare-haren daban-daban, amma daga bisani, jami’an tsaro da hadin gwiwar KadVS, sun kwato shanun.













