Iran da Amurka sun ƙara kai wa juna hare-hare a Gabas ta Tsakiya yayin da rikicin ya ƙara tsananta, musamman kan mashigar ruwan Hormuz, wadda ke da matuƙar muhimmanci wajen jigilar man fetur da iskar gas a duniya.
A ranar Laraba, Rundunar Kare Juyin Juya Halin Musulunci ta Iran (IRGC) ta ce ta kai hare-hare kan jiragen ruwan Amurka 20 da ke ƙoƙarin ratsa mashigar Hormuz.
Iran ta ce hare-haren martani ne ga farmakin da sojojin Amurka suka kai kan tankokin dakon man Iran guda biyar a ranar Talata.
Rundunar ta kuma ce ta kai hari kan wani sansanin sojin Amurka da ke Jordan, a matsayin ramuwar gayya kan hare-haren Amurka.
A nata bangaren, sojojin Amurka sun ce sun kai farmakin ne bayan Iran ta kai hari kan wani jirgin ruwan yaƙin Amurka, wanda shi ne hari na biyu makamancin haka cikin ƙasa da mako guda.
Rikicin ya shafe watanni shida, inda Iran ke ci gaba da hana zirga-zirgar jiragen ruwa yadda ya kamata a mashigar Hormuz, yayin da Amurka ke ƙoƙarin takura wa tashoshin jiragen ruwa da tattalin arzikin Iran.













