Ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomi da sakatarorin ƙungiyoyin jam’iyyar APC a Jihar Katsina ta bayyana cikakken goyon bayanta ga Gwamna Dikko Umaru Radda, bisa la’akari da yadda ya jagoranci jihar cikin shekaru uku da suka gabata.
An cimma wannan matsayar ne a ranar Talata, a zauren majalisar zartarwa na Gidan Muhammadu Buhari da ke Katsina, yayin da ƙungiyar ke miƙa rahoton rangadin da ta gudanar a mazabun tarayya 15 da ke jihar.
Shugaban ƙungiyar, Alhaji Salisu Mamman, ya ce gwamnatin Gwamna Radda ta samu ci gaba a fannonin ababen more rayuwa, ilimi, kiwon lafiya, noma da bunƙasa ɗan Adam.
Ya ce salon shugabancin gwamnan, wanda ya ginu kan gaskiya, riƙon amana da bai wa kowa dama, ya dawo da amincewar jama’a tare da kawo ci gaba zuwa matakin ƙananan hukumomi da al’umma.
Alhaji Mamman ya ƙara da cewa ƙungiyar ta miƙa wuya ga jagorancin gwamnan, tare da bayyana aniyarta ta ganin APC ta samu nasara a zaɓen 2027 a ƙarƙashin jagorancinsa.
Ya kuma gabatar da rahoton kwamitin da ya gudanar da rangadin, inda ya ce aikin ya ba su damar tattaunawa kai tsaye da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar a matakin ƙasa, tare da gano abubuwan da ke ƙarfafa haɗin kai da kuma ƙalubalen da ake fuskanta.
A cewarsa, dukkan ƙananan hukumomi 34 na jihar suna da kwamitocin tuntuɓa da gangamin jama’a masu aiki a matakan ƙaramar hukuma, mazabu da rumfunan zaɓe, ciki har da tsare-tsaren da suka shafi matasa, mata da dattawa.
Ya kuma bayyana wasu muhimman batutuwan da aka gabatar yayin rangadin, inda ya buƙaci gwamnan da ya duba shawarwarin tare da amfani da su a matsayin taswira wajen ƙarfafa jam’iyyar gabanin zaɓe.
A nasa jawabin, Gwamna Dikko Umaru Radda ya gode wa masu ruwa da tsakin bisa biyayyarsu, jajircewarsu da sadaukarwarsu ga jam’iyyar.
Gwamnan ya yaba musu bisa gudanar da rangadin tare da samar da sahihin bayani daga matakin ƙasa, yana mai cewa irin wannan hulɗa na da matuƙar muhimmanci wajen ƙarfafa APC.
Ya kuma buƙace su da su tabbatar da haɗin kan da ya kasance alamar jam’iyyar zuwa zaɓen 2027. Ya yi kira gare su da su ƙara himma wajen tattara jama’a domin ganin an sake zaɓar Shugaba Bola Ahmed Tinubu, da kuma dukkan ’yan takarar APC a Jihar Katsina.
Ya ce samun nasara a zaɓen na buƙatar haɗin kai da aiki tare.
Taron ya samu halartar Shugaban Ma’aikatan Gwamna, Hon. Abdulkadir Mamman Nasir; Kwamishinan Filaye da Tsare-tsaren Birane, Dr. Faisal Kaita; Mai Ba Gwamna Shawara kan Harkokin Siyasa, Hon. Yau Umar Gwajo-Gwajo, da Mai Ba Gwamna Shawara kan Hulɗa da Jam’iyya, Hon. Shafiu Abdu Duwan.














