ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Burin Sin Na Tabbatar Da Zaman Lafiya A Duniya Bai Sauya Ba

by CGTN Hausa
3 years ago
Sin

Yanzu haka dai hankalin duniya ya karkata ne ga rikicin dake faruwa tsakanin Palasdinu da Isra’ila, inda duk wayewar gari rayuka ke salwanta tsakanin bangarorin biyu.

Kuma tun kafin ta zama shugabar karba-karba ta kwamitin sulhun MDD, kasar Sin ke ta kira tare da gabatar da matakai a lokuta daban-daban, na kawo karshen tashe-tashen hankulan dake faruwa a sassan duniya. Sannan bayan da ta karbi shugabancin karba-karba na kwamitin sulhun MDD, kasar Sin ta jaddada kudurinta na ci gaba da yin hadin gwiwa da bangarorin da abin ya shafa, wajen sa kaimi ga kwamitin sulhu na MDD na daukar matakan da suka dace na tsagaita bude wuta, da kawo karshen yaki, da rage yanayin jin kai da ake ciki, da taka rawar da ta dace wajen samar da zaman lafiya mai dorewa tsakanin Falasdinu da Isra’ila ta hanyar “shirin kafa kasashe biyu”.

  • Darajar Cinikayyar Kasar Sin A Ketare Ya Karu Da Kaso 0.03% Cikin Watanni 10 Na Bana
  • Kwamishinan Cinikayya Da Zuba Jari Na Najeriya Dake Shanghai Ya Yaba Da Manufofin Kasar Sin Na Fadada Bude Kofa Ga Kasashen Waje

Sin na kara bayyana cewa, wajibi ne kasashen duniya su dauki matakin gaggawa, kuma kasashen dake wajen yankin, musamman ma manyan kasashe, su tabbatar da gaskiya da adalci, tare da taka rawa mai ma’ana wajen ganin an sassauta yanayin da ake ciki.

ADVERTISEMENT

Idan ba a manta a ranar 1 ga watan Nuwamba, lokacin da kasar Sin ta karbi wannan shugabanci, zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Zhang Jun ya bayyana cewa, halin da ake ciki tsakanin Falasdinu da Isra’ila shi ne batu mafi muhimmanci a ajandar kwamitin sulhu na wannan wata. Kana aikin dake kan gaba shi ne karfafa maganar tsagaita bude wuta da kawo karshen yakin, da hana karin asarar rayukan fararen hula, bala’un jin kai, da rikice-rikice.

Kamar kullum Sin na Allah wadai da duk wasu matakai na muzgunawa, da kaiwa fararen hula hare-hare, domin rayukan al’umma na da matukar alfarma, kuma bai dace tashin hankalin da ake fama da shi ya haifar da salwantar rayukan fararen hula Falasdinawa ko Isra’ilawa ba.

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Sin mai kaunar zaman lafiya na kira da a gaggauta komawa teburin shawarwari, domin kaiwa ga cimma matsaya, dangane da aiwatar da manufar nan ta warware riciki ta hanyar kafa kasashe biyu masu cin gashin kai, a kuma shata matakai daki-daki na cimma nasarar hakan.

Kuma a matsayinta na shugabar kwamitin sulhu na majalisar na wannan karo, kasar Sin za ta yi biyayya ga kiraye-kirayen kasashen duniya, da yin aiki tare da bangarorin da abin ya shafa, wajen sa kaimi ga kwamitin don daukar matakai na bai daya masu ma’ana cikin lokaci.

Wannan ya kara nunawa duniya cewa, kasar Sin tun fil-azal, kasa ce mai kaunar zaman lafiya ba neman tashin hankali ba. Sabanin wasu kasashe dake amfani da matsayi ko ikonsu na kara rura wutar fitina, ba tare da la’akari da rayukan dake salwanta ba. Domin zaman lafiya ya fi zama dan Sarki. (Ibrahim Yaya)

 

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

MASU ALAKA

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Next Post
Gwamnatin Kaduna Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Kudancin Jihar Da Suka Bar Matsugunansu

Gwamnatin Kaduna Za Ta Sake Tsugunar Da 'Yan Kudancin Jihar Da Suka Bar Matsugunansu

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
Sin

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Sin

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026
Sin

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.