A yau Lahadi ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya mikawa shugaban kasar Maldives Mohamed Muizzu, sakon murnar cika shekaru 61 da samun ‘yancin kan kasar.
A cikin sakon nasa, shugaba Xi ya yi nuni da cewa, Sin da Maldives sun sada zumunta a dogon lokaci. A cikin shekaru 54 da kulla dangantakar diplomasiyya a tsakaninsu, kasashen biyu sun raya dangantakar abokantaka bisa tushen ka’idoji 5 na zaman tare cikin lumana, wanda hakan ya haifar da moriya ga jama’arsu.
Ya ce a yayin da shugaban Maldives Mohamed Muizzu ya kawo ziyara kasar Sin a shekarar 2024, kasashen biyu sun amince da inganta dangantakarsu, zuwa dangantakar abokantaka ta hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni, da raya makomar bai daya ta al’ummar kasashen biyu.
Shugaba Xi, ya ce yana fatan yin kokari tare da shugaba Muizzu, wajen kara sada zumunta, da zurfafa hadin gwiwarsu, don sa kaimi ga raya dangantakar abokantaka ta hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni, ta yadda hakan zai amfani jama’arsu baki daya.
A wani ci gaban kuma, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, shi ma ya mikawa takwararsa ta kasar Maldives Iruthisham Adam, sakon murnar cika shekaru 61 da samun ‘yancin kan kasar. (Zainab Zhang)














