Wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun yi garkuwa da Alƙalin Babbar Kotun Jihar Kebbi, Mai Shari’a Faruku Hassan Bunza, a gidansa da ke kan titin Zogirma a ƙaramar hukumar Bunza.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 12:00 na dare, jim kaɗan bayan Alƙalin ya dawo daga wata tafiya zuwa jihar Sakkwato. Maharan sun yi ta harbe-harbe domin firgita mazauna yankin kafin su tafi da shi. Babu wani rahoton jikkata daga cikin iyalansa ko maƙwabta.
Wata majiya daga cikin iyalansa ta ce an kai rahoton lamarin ga hukumomin tsaro da kuma shugabancin Babbar Kotun Jihar Kebbi. Ta kuma yi kira ga gwamnati da jami’an tsaro su gaggauta ceto Alƙalin cikin ƙoshin lafiya.
Wani babban jami’in kotun da ya nemi a sakaya sunansa ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa shugabannin kotun sun fara tuntubar hukumomin tsaro domin tabbatar da an kuɓutar da alkalin cikin gaggawa.
Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar Kebbi, SP Bashir Usman, ya kuma tabbatar da sace alkalin. Ya ce Kwamishinan ‘Yansanda na jihar, CP Umar Muhammad Hadijeja, ya tura jami’an leƙen asiri da na musamman domin farautar maharan da ceto Mai Shari’a Faruku Hassan Bunza.
Rundunar ta ce ana ci gaba da gudanar da bincike tare da sintiri a yankunan da ake zargin maharan za su iya ɓuya, yayin da har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto babu wata ƙungiya da ta ɗauki alhakin harin.














