ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

by Umar Faruk Birnin Kebbi and Abubakar Sulaiman
6 hours ago

Wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun yi garkuwa da Alƙalin Babbar Kotun Jihar Kebbi, Mai Shari’a Faruku Hassan Bunza, a gidansa da ke kan titin Zogirma a ƙaramar hukumar Bunza.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 12:00 na dare, jim kaɗan bayan Alƙalin ya dawo daga wata tafiya zuwa jihar Sakkwato. Maharan sun yi ta harbe-harbe domin firgita mazauna yankin kafin su tafi da shi. Babu wani rahoton jikkata daga cikin iyalansa ko maƙwabta.

Wata majiya daga cikin iyalansa ta ce an kai rahoton lamarin ga hukumomin tsaro da kuma shugabancin Babbar Kotun Jihar Kebbi. Ta kuma yi kira ga gwamnati da jami’an tsaro su gaggauta ceto Alƙalin cikin ƙoshin lafiya.

ADVERTISEMENT

Wani babban jami’in kotun da ya nemi a sakaya sunansa ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa shugabannin kotun sun fara tuntubar hukumomin tsaro domin tabbatar da an kuɓutar da alkalin cikin gaggawa.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar Kebbi, SP Bashir Usman, ya kuma tabbatar da sace alkalin. Ya ce Kwamishinan ‘Yansanda na jihar, CP Umar Muhammad Hadijeja, ya tura jami’an leƙen asiri da na musamman domin farautar maharan da ceto Mai Shari’a Faruku Hassan Bunza.

LABARAI MASU NASABA

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

Rundunar ta ce ana ci gaba da gudanar da bincike tare da sintiri a yankunan da ake zargin maharan za su iya ɓuya, yayin da har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto babu wata ƙungiya da ta ɗauki alhakin harin.

Umar Faruk Birnin Kebbi
+ posts Bio
  • Umar Faruk Birnin Kebbi
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-birnin-kebbi/
    Kungiyar Malaman Jami’ar AFUSTA Za Ta Tsunduma Yajin Aiki
  • Umar Faruk Birnin Kebbi
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-birnin-kebbi/
    An Cafke Matar Da Ta Binne Jariri Da Rai A Kebbi
  • Umar Faruk Birnin Kebbi
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-birnin-kebbi/
    Gwamnatin Kebbi Ta Ba da Ƙwangilar Gina Hanyoyi Kan Naira Biliyan 2.1
  • Umar Faruk Birnin Kebbi
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-birnin-kebbi/
    Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi
Abubakar Sulaiman
Website |  + posts Bio
  • Abubakar Sulaiman
    Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata
  • Abubakar Sulaiman
    Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara
  • Abubakar Sulaiman
    Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe
  • Abubakar Sulaiman
    Ku Buɗe Wuta Kan Duk Wanda Kuka Gani Ɗauke Da Bindiga – IGP

MASU ALAKA

Manyan Labarai

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Labarai

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Bala Mohammed
Labarai

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026
Next Post
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

LABARAI MASU NASABA

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026
Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.