Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya naɗa Dr. Wasiu Olanrewaju-Smart a matsayin Mai Ba da Shawara na Musamman kan Harkokin Majalisar Dokokin Ƙasa (Majalisar Wakilai). Naɗin ya zo ne bayan murabus ɗin Ibrahim Olanrewaju, wanda ya ajiye muƙaminsa domin neman takarar zaɓe a jiharsa.
Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya bayyana cewa Dr. Olanrewaju-Smart ƙwararre ne a fannin manufofin gwamnati da ilimi. Yana da digirin digirgir a fannin Gudanar da Ilimi daga Lead City University, da kuma digirin Master’s a fannin Gudanar da Harkokin Jama’a daga Jami’ar Harvard.
Sanarwar ta ce ya taɓa zama mataimaki kan bincike da yaɗa labarai ga shugabannin marasa rinjaye da masu rinjaye a Majalisar Wakilai ta bakwai da ta takwas. Daga bisani kuma ya riƙe muƙaman Mai Ba da Shawara na Musamman, da Mataimakin Babban Hafsan Ofis da Babban Hafsan Ofis ga Kakakin Majalisar Wakilai a majalisu ta tara da ta goma.
Tun daga watan Oktoban 2023, Dr. Olanrewaju-Smart ke aiki a Fadar Shugaban Ƙasa a matsayin Babban Mataimaki na Musamman kan Hulɗa da Gwamnatocin Jihohi. Haka kuma, binciken da ya gudanar kan manufofin gwamnati ya taimaka wajen samar da wasu muhimman dokoki, ciki har da Dokar Ba da Rancen Karatu Ba Tare da Riba ba.
Shugaba Tinubu ya bayyana ƙwarin gwiwarsa cewa sabon mai ba da shawarar zai ƙara inganta haɗin gwuiwa tsakanin Fadar Shugaban Ƙasa, da ma’aikatu, da hukumomi da Majalisar Wakilai. Sanarwar ta ce naɗin ya fara aiki nan take.














