ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

by Abubakar Sulaiman
2 hours ago

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya naɗa Dr. Wasiu Olanrewaju-Smart a matsayin Mai Ba da Shawara na Musamman kan Harkokin Majalisar Dokokin Ƙasa (Majalisar Wakilai). Naɗin ya zo ne bayan murabus ɗin Ibrahim Olanrewaju, wanda ya ajiye muƙaminsa domin neman takarar zaɓe a jiharsa.

Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya bayyana cewa Dr. Olanrewaju-Smart ƙwararre ne a fannin manufofin gwamnati da ilimi. Yana da digirin digirgir a fannin Gudanar da Ilimi daga Lead City University, da kuma digirin Master’s a fannin Gudanar da Harkokin Jama’a daga Jami’ar Harvard.

Sanarwar ta ce ya taɓa zama mataimaki kan bincike da yaɗa labarai ga shugabannin marasa rinjaye da masu rinjaye a Majalisar Wakilai ta bakwai da ta takwas. Daga bisani kuma ya riƙe muƙaman Mai Ba da Shawara na Musamman, da Mataimakin Babban Hafsan Ofis da Babban Hafsan Ofis ga Kakakin Majalisar Wakilai a majalisu ta tara da ta goma.

ADVERTISEMENT

Tun daga watan Oktoban 2023, Dr. Olanrewaju-Smart ke aiki a Fadar Shugaban Ƙasa a matsayin Babban Mataimaki na Musamman kan Hulɗa da Gwamnatocin Jihohi. Haka kuma, binciken da ya gudanar kan manufofin gwamnati ya taimaka wajen samar da wasu muhimman dokoki, ciki har da Dokar Ba da Rancen Karatu Ba Tare da Riba ba.

Shugaba Tinubu ya bayyana ƙwarin gwiwarsa cewa sabon mai ba da shawarar zai ƙara inganta haɗin gwuiwa tsakanin Fadar Shugaban Ƙasa, da ma’aikatu, da hukumomi da Majalisar Wakilai. Sanarwar ta ce naɗin ya fara aiki nan take.

LABARAI MASU NASABA

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi
  • Abubakar Sulaiman
    Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe
  • Abubakar Sulaiman
    Ku Buɗe Wuta Kan Duk Wanda Kuka Gani Ɗauke Da Bindiga – IGP

MASU ALAKA

Manyan Labarai

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed
Labarai

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

LABARAI MASU NASABA

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026
Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.