Yanzu haka saura kusan kwanaki 100 a bude gasar wasannin Olympics ta matasa ta birnin Dakar ta shekarar 2026, kuma kasar Senegal dake yammacin nahiyar Afirka, ke ci gaba da shirin karbar bakuncin gasar.
A jiya Asabar 25 ga wannan wata, shugaban kasar Senegal Bassirou Diomaye Faye, ya ziyarci filin wasa na Diop dake birnin Dakar, da sauran zaurukan gudanar da wasannin gasar, inda ya jinjinawa kasar Sin bisa kwazon kammala ginawa, da gyara zaurukan da za a yi amfani da su yayin gasar a kan lokaci.
Filin wasa na Diop, yana daya daga cikin manyan filayen wasa na gudanar da gasar ta Olympics ajin matasa ta Dakar ta shekarar 2026, kuma akwai bukatar kammala gyaran shi gabanin bude gasar. Kamfanonin Sin shiga ayyukan gyaran filin, ciki har da cire dandalin zaman ‘yan kallo, da sake gini da fadada dandalin wasa. Kana an gyara da sake gina filin wasan kwallon kwando, da na wasan kwallon hannu, da na wasan kwallon raga, tare da inganta dakunan wasannin motsa jiki, da na horaswa, da wuraren kwanciya, da hanyoyin mota, da kofofin shiga da na fita, da wuraren ajiye mota a dukkanin sassan filin baki daya.
Kammala aikin zai inganta karfin ayyukan wasannin motsa jiki na birnin Dakar, da samar da yanayi mai kyau na gudanar da gasar, da horas da ‘yan wasa mahalarta gasar wasannin na Olympics ajin matasa.
Za a gudanar da gasar wasannin Olympics ta matasa ta Dakar ta shekarar 2026, tun daga ranar 31 ga watan Oktoba zuwa 11 ga watan Nuwanba, kuma wannan ne karo na farko da gasar ta matasa za ta gudana a nahiyar Afirka, kana gasar wasannin Olympics ta farko da za a gudanar a nahiyar Afirka a tarihi. (Zainab Zhang)













