ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Mai Burin Ganin Ci Gaban Kowa

by CGTN Hausa
3 years ago
Kasar Sin

Da safiyar yau Talata, ofishin watsa labarai na majalisar gudanarwar kasar Sin ya gabatar da takardar bayani mai taken “Al’ummar duniya mai makoma ta bai daya: Shawara da matakan kasar Sin,” wadda ta yi cikakken bayani game da yadda za a karfafa dunkulewar dukkanin bil adama. 

Takardar ta tabo wasu muhimman batutuwa da suka ja hankalina, nake ganin ya kamata al’ummar kasa da kasa su fahimta dangane da shawarar gina kyakkyawar makomar bil adama ta bai daya.

  • Juan Antonio Samaranch Jr.: Shugaba Xi Muhimmin Abokin Tafiya Ne Na Gasar Olympic
  • Xi Ya Yi Kira Ga Lardin Zhejiang Da Ya Rubuta Sabon Babi Na Inganta Zamanantarwa Ta Sin

Na farko: Gabatar da sabuwar dabarar huldar diflomasiyya. Tabbas huldar kasa da kasa na cikin wani yanayi mai wuyar fahimta. Maimakon hada kai da zama masu ceton juna, sai ake fuskantar rarrabuwar kawuna da neman samun nasara daga faduwar wata kasa. Abubuwa da dama sun riga sun nuna mana cewa, babu wata kasa da za ta iya shawo kan kalubalen duniya ita kadai. A wannan gaba, takardar ta Sin ta nemi kasa da kasa su yi la’akari da cewa makomarsu na hade da juna, don haka kamata ya yi su hade kansu domin samun moriyar juna. Hakika, wannan ita ce hanya daya tilo mai bullewa, domin dabaru na mulkin danniya da babakere, ba su amfani duniyarmu da komai ba sai fitina da rashin zaman lafiya da talauci da sauransu.

ADVERTISEMENT

Na biyu: Samar da sabbin dabarun shugabantar duniya.

A cewar takardar, makoma ta bai daya ta bil adama, ita ce samun duniya mai daidaito da adalci da gaskiya. Hakika dukkanin bil adama ba su da bambanci. Misali, a lokacin annobar COVID-19, annobar ba ta kama mutane bisa launi ko addini ko kabilarsu ba. Wannan na kara tabbatar da cewa, babu wanda da ya fi wani. Haka kuma babu wata kasa da ta fi wata. Don haka bai kamata wata ko wasu ’yan tsiraru su wa duniya babakere ko su rika cin zalin wasu ba. Manufar kasar Sin ita ce, a tabbatar da daidaito da adalci da tsare gaskiya domin a gudu tare a tsira tare, a kuma kai ga samun duniya mai makoma ta bai daya ga dukkan bil adama.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Na uku: samar da sabbin damarmakin musaya tsakanin kasa da kasa.

Kamar yadda Mal. Bahaushe kan ce, “Hannu daya ba ya daukar jinka”, shawarar kasar Sin a nan ita ce, inganta cudanyar kasa da kasa bisa daidaito da adalci da musaya tsakanin al’ummominsu. Babban abun dake kawo sabani, a ganina shi ne, rashin fahimta. Inganta musaya tsakanin al’ummomin kasa da kasa tabbas zai kara fahimtar da juna game da al’adu da dabi’u da yanayin juna. Haka kuma, musaya da hadin gwiwa tsakanin kasa da kasa zai bude wata sabuwar kafa ta samun ci gaba da koyi da juna, lamarin da zai sa kasashe su kasance masu mayar da hankali kan ci gaban juna maimakon neman ganin faduwarsu.

Na hudu: Gudunmawa da matakan kasar Sin.

A nan takardar ta kuma zayyano wasu daga cikin gudunmawar kasar Sin wajen cimma wannan buri, kamar shawarar Ziri Daya da Hanya Daya, shawarar ci gaban duniya, shawarar tsaron duniya, shawarar warware matsalar Ukraine da Rasha da sauransu. Wadannan duka shawarwari ne da kasar Sin ta gabatar da zummar kai wa ga samar da kyakkyawar makomar bil adama.

Wadannan batutuwa kadan ne daga cikin abubuwan da wannan takarda ta kunsa. Tabbas kasar Sin ba ta tsaya kan rayawa da neman inganta kanta. Har kullum, ba ta nuna son kai ko girman kai, burinta shi ne, ganin dukkan kasashen duniya sun samu ci gaba da zaman lafiya ta yadda bil adama za su yi zaman jituwa cikin wadata da kwanciyar hankali. Wannan ita ake kira da babbar kasar mai sowa kowa abun da take sowa kanta.

Kasar Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Kungiyar Kwadago (NLC) Na Shirin Tsunduma Wani Sabon Yajin Aiki Mai Dogon Zango

NLC Da TUC Sun Shirya Tsunduma Yajin Aiki Mai Dogon Zango Ranar Talata 3 Ga Oktoba 2023

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.