A halin yanzu, ciwon ido mai saurin yaɗuwa wato ‘Apollo’ ta kama Kakakin Majalisar Dokokin jihar Bauchi, Abubakar Y. Sulaiman.
Kakakin Majalisar ne ya tabbatar da kamuwa da cutar da kansa inda ya wallafa a shafinsa na facebook a jiya Lahadi.
Ya kuma shaida cewar, a halin yanzu cutar tana nan tana yaɗuwa a jihar don haka ne ya nemi jama’a da su ɗauki matakan kariya ciki har da kula da tsafta.
Ya wallafa da cewa, “Cikin ikon Allah, yau na tashi da ciwon ido mai saurin yaɗuwa, wadda aka fi sani da “Apollo,” kuma a halin yanzu tana yaɗuwa a faɗin jihar Bauchi.
“Ina kira ga kowa da kowa da ya kasance cikin taka-tsantsan, ya kula da tsafta, tare da ɗaukar matakan kariya da suka dace domin hana cutar ƙara yaɗuwa a tsakanin al’umma. Allah uban giji ya kawo mana sauki Na gode,” ya wallafa.














