ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

by Rabi'u Ali Indabawa
42 minutes ago
Abinci

Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya ta bayyana a ranar Litinin cewa Nijeriya na samun kusan mutum miliyan 50 da ke kamuwa da cututtukan da ke da alaka da gurbataccen abinci, yayin da sama da mutum 53,000 ke mutuwa sakamakon irin wadannan cututtuka a duk shekara.

Karamin Ministan Lafiya da Jin Dadin Jama’a, Iziak Salako, ne ya bayyana hakan a Abuja yayin wani taron manema labarai domin tunawa da Ranar Kula da Tsaron Abinci ta Duniya ta shekarar 2026.

Ya bukaci masana’antun sarrafa abinci da su sake duba kayayyakinsu ta hanyar rage gishiri, sukari da kitse marasa lafiya, tare da inganta tsafta, bin diddigin kayayyaki da bayyana sahihan bayanai a jikin kayan abinci domin rage yawaitar cututtukan da ke da alaka da abinci a kasar.

ADVERTISEMENT

Salako ya ce yara masu shekaru kasa da biyar ne ke daukar sama da kashi 80 cikin 100 na nauyin cututtukan da ke fitowa daga gurbataccen abinci a Nijeriya, yana mai gargadin cewa rashin ingancin abinci na lalata lafiya, ci gaba da kuma makomar miliyoyin yara a kasar.

A cewarsa, sama da mutum miliyan 40 na kamuwa da gudawa a Nijeriya na da alaka da kwayoyin cuta da ke cikin abinci kamar Salmonella infection, Escherichia coli infection, Campylobacter, Shigella da rotabirus. Ya kuma ce gurbatattun sinadarai, ciki har da gubar lead, na zama babbar barazana ga lafiyar jama’a.

LABARAI MASU NASABA

Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

Ministan ya jaddada cewa bai kamata a ci gaba da kallon tsaron abinci a matsayin batun fasaha kawai ba, sai dai a matsayin wani muhimmin batu na tsaron lafiya da ci gaban kasa.

Ya kara da cewa baya ga hana yaduwar cututtuka, dole ne tsaron abinci ya kuma magance yawaitar cututtukan da ba sa yaduwa daga mutum zuwa mutum kamar Hypertension, Stroke, Diabetes, Obesity da cututtukan zuciya, wadanda ke da alaka da yawan amfani da gishiri, sukari da kitse masu illa ga lafiya.

Salako ya bayyana cewa National Agency for Food and Drug Administration and Control ta kammala shirya dokokin rage sinadarin sodium a cikin abincin da ake sarrafawa, yayin da Nijeriya ke aiwatar da dokokin kawar da kitse na masana’antu (trans fats) bisa shawarwarin Hukumar Lafiya ta Duniya.

Ya kuma kara da cewa gwamnati na karfafa harajin abubuwan sha masu yawan sukari tare da samar da tsarin bayyana bayanan sinadaran abinci a gaban marufi, domin bai wa masu amfani da kayayyakin abinci damar yin zabi mafi inganci ga lafiyarsu.

Ministan ya kuma yi kira ga masu sayar da abinci da masu gudanar da harkokin kasuwanci da su bi ka’idojin kasa na tsaron abinci, tare da rokon abokan huldar ci gaba, masu bincike da kafafen yada labarai da su mara wa kokarin inganta sa ido, wayar da kan jama’a da kuma kyawawan hanyoyin tabbatar da amincin abinci baya.

A cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Litinin domin tunawa da Ranar Tsaron Abinci ta Duniya ta 2026, CAPPA ta yi gargadin cewa miliyoyin ’yan Nijeriya na kara fuskantar hadarin lafiya sakamakon yawan amfani da sukari, gishiri, kitse marasa lafiya da kuma abincin da aka sarrafa fiye da kima.

Babban Daraktan CAPPA, Akinbode Oluwafemi, ya ce: “Tsaron abinci ba wai kawai hana gubar abinci ba ne. Haka kuma yana nufin tabbatar da cewa abinci da abubuwan sha da ake samarwa ’yan Nijeriya ba sa lalata lafiyarsu da jin dadinsu a hankali.”

Ya yi gargadin cewa raunin matakan kariya na doka da kuma tallata kayayyakin da ba su da amfani ga lafiya cikin karfi na taimakawa wajen karuwar masu fama da Hypertension, Diabetes, Obesity, Stroke, cututtukan koda da kuma wasu nau’o’in cutar daji.

Abinci
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Samar Da Abinci:Jihar Nasarawa Ta Fara Shirin Gina Kananan Madatsun Ruwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

MASU ALAKA

Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare
Labarai

Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare

June 12, 2026
Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

June 12, 2026
Samar Da Abinci:Jihar Nasarawa Ta Fara Shirin Gina Kananan Madatsun Ruwa
Labarai

Samar Da Abinci:Jihar Nasarawa Ta Fara Shirin Gina Kananan Madatsun Ruwa

June 12, 2026

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026
Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare

Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare

June 12, 2026
Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.