Alamu masu karfi sun nuna a ranar Juma’a cewa adadin kujerun Majalisar Dokokin Tarayya na iya karuwa sakamakon wani kudirin gyaran kundin tsarin mulki da ke da nufin kara yawan wakilcin mata a harkokin mulki.
A karkashin kudirin, adadin kujerun Majalisar Dattawa zai karu daga 109 zuwa 121, yayin da na Majalisar Wakilai zai tashi daga 360 zuwa 397, idan aka fara aiwatar da shi daga babban zaben shekarar 2027.
Sabbin kujeru 12 na Majalisar Dattawa da kuma kujeru 37 na Majalisar Wakilai za a tanade su ne musamman domin mata. Ba za a zabe su ta hanyar babban zabe ba, sai dai ta hanyar naɗi (Electoral College) a shiyyoyin siyasa shida, jihohi 36 da Babban Birnin Tarayya (FCT).
Kudirin ya sake samun goyon baya a wani taron shiyyar da Kungiyar Mata Masu Zabe ta Nijeriya (NILOWV) ta shirya tare da masu daukar nauyin kudurorin da ke neman ware kujeru na musamman ga mata a Majalisar Dokoki.
Daya daga cikin masu daukar nauyin kudirin, Hon. Iduma Igariwey Enwo, ya bayyana cewa shugabannin majalisun biyu na Majalisar Dokokin Tarayya suna nuna goyon baya ga kudirin, amma ya jaddada cewa har yanzu ana bukatar ci gaba da gudanar da yakin neman goyon baya domin tabbatar da amincewa da shi.














