ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, September 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Radda Ya Kaddamar da Tattaunawar Kasafin Kuɗin 2027

by Sulaiman
2 months ago
Radda

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya ƙaddamar da zagaye na biyu na tarukan tattaunawa a matakin mazabu domin shirya kasafin kuɗin jihar na shekarar 2027, inda ya sake jaddada kudirin gwamnatinsa na tabbatar da shigar da al’umma cikin harkokin mulki.

Mai magana da yawun Gwamnan Jihar Katsina, Ibrahim Kaula Mohammed ne ya bayyana haka acikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar 18 ga watan Yuli, 2026.

Ya bayyana cewa, an ƙaddamar da shirin ne a Mazaɓar Radda da ke Ƙaramar Hukumar Charanchi, yayin da aka gudanar da irin wannan tattaunawa lokaci guda a dukkan mazabu 361 da ke ƙananan hukumomi 34 na jihar.Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Radda ya bayyana cewa tattaunawar ci gaba ce na alkawarin da gwamnatinsa ta ɗauka na sanya jama’a a cikin tsarin mulki. Ya ce kowace al’umma ta cancanci a saurare ta, kuma gudummawar mazauna jihar na da matuƙar muhimmanci wajen tsara manufofin gwamnati da kuma makomar ci gaban Jihar Katsina.

ADVERTISEMENT

Gwamnan ya tuna cewa tattaunawar farko da aka gudanar kafin shirya kasafin kuɗin shekarar 2026 ta kafa tarihi, domin a karon farko al’ummar dukkan mazabu 361 sun samu damar ba da tasiri kai tsaye wajen tsara ayyukan gwamnati. Ya bayyana cewa da dama daga cikin shawarwarin da aka tattara a wancan lokaci sun zama ayyukan raya ƙasa da ake aiwatarwa a fannoni kamar gine-ginen tituna, lafiya, ilimi, noma, samar da ruwan sha, ƙarfafa matasa, walwalar jama’a, ci gaban al’umma da kuma tallafa wa harkokin tsaro.

Gwamna Radda ya amince cewa duk da ƙarancin albarkatun gwamnati, ba a yin watsi da buƙatun al’umma na gaskiya. Ya bayyana cewa duk shawarwarin da ba za a iya aiwatar da su nan take ba ana adana su domin la’akari da su a kasafin kuɗi na gaba ko wasu shirye-shiryen gwamnati. Haka kuma ya bukaci al’umma su riƙa sa ido kan yadda ake aiwatar da ayyuka domin ƙarfafa gaskiya, riƙon amana da kuma tabbatar da amfani mai kyau da kuɗaɗen jama’a.Ya kuma ƙarfafa gwiwar mazauna jihar da su shiga tattaunawar tare da gabatar da ayyuka masu ma’ana da za su magance manyan matsalolin al’ummominsu. Musamman ya yi kira ga matasa, mata, masu buƙata ta musamman, manoma, ‘yan kasuwa, masu sana’o’i da ƙungiyoyin al’umma da su yi amfani da wannan dama, yana mai jaddada cewa ci gaba mai ɗorewa ba zai samu ba sai da haɗin gwiwa tsakanin gwamnati da jama’a.

LABARAI MASU NASABA

Motoci Masu Amfani Da CNG Da Lantarki Sun Rage Kuɗin Sufuri Da Kashi 83 – Tinubu

Yadda Ƴan Bindiga Suka Kashe Ƴan Kasuwa 3 A Filato

Tun da farko, Kwamishinan Kasafi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki, Alhaji Malik Anas, ya ce gwamnatin Radda ta kafa tarihi ta hanyar gudanar da tattaunawar kasafin kuɗi a dukkan mazabu 361 kafin kasafin kuɗin shekarar 2026. Ya tabbatar wa mahalarta taron cewa za a rubuta, a tantance tare da haɗa dukkan shawarwarin da aka samu cikin tsarin tsare-tsaren gwamnati gwargwadon albarkatun da ake da su da kuma abubuwan da gwamnati ta bai wa fifiko.

Ya kuma bukaci jama’a su mayar da hankali kan ayyuka masu amfani da za su inganta rayuwar al’umma.Shi ma Mai Kula da Shirin Ci Gaban Al’umma (CDP), Dakta Kamaludeen Kabir, ya sake jaddada cewa ci gaba mai ɗorewa ba zai tabbata ba sai idan al’umma da kansu sun gano abubuwan da suka fi buƙata kuma suka shiga cikin yanke shawarar da ta shafi rayuwarsu.

Ya bayyana cewa shirin CDP ya tura jami’ansa zuwa matakin ƙasa domin jagorantar tattaunawar, tattara buƙatun al’umma da tabbatar da cewa an haɗa dukkan shawarwarin da suka dace cikin shirye-shiryen kasafin kuɗin shekarar 2027.

An shirya tarukan ne ƙarƙashin jagorancin Ma’aikatar Kasafi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki tare da haɗin gwiwar Shirin Ci Gaban Al’umma (CDP) ƙarƙashin taken “Building Your Future IV.” Manufar shirin ita ce bai wa al’ummar dukkan mazabu 361 damar taka rawa kai tsaye wajen tsara kasafin kuɗin Jihar Katsina na shekarar 2027.

Taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, sarakunan gargajiya da na addini, wakilan al’umma da sauran masu ruwa da tsaki, lamarin da ya sake nuna kudirin gwamnatin Radda na tabbatar da shugabanci mai haɗa kowa da kowa, gaskiya, riƙon amana da ci gaban da jama’a ke jagoranta.

Radda
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Angola: Kasar Sin Tana Da Shugaba Mai Hangen Nesa
  • Sulaiman
    Yadda Amurka Ta Mayar Wa Sin Da Kayan Tarihi Ya Nuna Kyakkyawan Fata Na Gina Dangantaka Mai Inganci A Tsakaninsu
  • Sulaiman
    Sin Ta Bukaci Japan Ta Fuskanci Tarihinta Na Mamayar Zalunci Tare Da Waiwaye Mai Zurfi A Kai
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Samu Jarin Waje Kimanin Yuan Biliyan 479.95 A Watanni 8 Na FarkonBana

MASU ALAKA

Motoci Masu Amfani Da CNG Da Lantarki Sun Rage Kuɗin Sufuri Da Kashi 83 – Tinubu
Manyan Labarai

Motoci Masu Amfani Da CNG Da Lantarki Sun Rage Kuɗin Sufuri Da Kashi 83 – Tinubu

September 19, 2026
Yadda Ƴan Bindiga Suka Kashe Ƴan Kasuwa 3 A Filato
Labarai

Yadda Ƴan Bindiga Suka Kashe Ƴan Kasuwa 3 A Filato

September 19, 2026
Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 12, Sun Ceto Mutane 66 Da Aka Yi Garkuwa Da Su
Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 12, Sun Ceto Mutane 66 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

September 19, 2026
Next Post
Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

LABARAI MASU NASABA

Motoci Masu Amfani Da CNG Da Lantarki Sun Rage Kuɗin Sufuri Da Kashi 83 – Tinubu

Motoci Masu Amfani Da CNG Da Lantarki Sun Rage Kuɗin Sufuri Da Kashi 83 – Tinubu

September 19, 2026
Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Angola: Kasar Sin Tana Da Shugaba Mai Hangen Nesa

Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Angola: Kasar Sin Tana Da Shugaba Mai Hangen Nesa

September 19, 2026
2027: Magoyin Bayan Atiku Ya Fice Daga ADC, Ya Goyi Bayan Tinubu

2027: Magoyin Bayan Atiku Ya Fice Daga ADC, Ya Goyi Bayan Tinubu

September 19, 2026
Yadda Ƴan Bindiga Suka Kashe Ƴan Kasuwa 3 A Filato

Yadda Ƴan Bindiga Suka Kashe Ƴan Kasuwa 3 A Filato

September 19, 2026
Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 12, Sun Ceto Mutane 66 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 12, Sun Ceto Mutane 66 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

September 19, 2026
An Dakatar Da Jami’an NSCDC 21 Kan Mutuwar Masu Haƙar Ma’adinai A Neja

An Dakatar Da Jami’an NSCDC 21 Kan Mutuwar Masu Haƙar Ma’adinai A Neja

September 19, 2026
Ku Rage Farashin Mai, Ku Sakarwa Ƴan Nijeriya Mara – Atiku Ga Tinubu

Ku Rage Farashin Mai, Ku Sakarwa Ƴan Nijeriya Mara – Atiku Ga Tinubu

September 19, 2026
Portugal Ta Gayyaci Ronaldo Gasar UEFA Nations League

Portugal Ta Gayyaci Ronaldo Gasar UEFA Nations League

September 19, 2026
Hannun Jarin Matatar Dangote Ya Buɗe Wa Ƴan Nijeriya Ido – FCMB

Hannun Jarin Matatar Dangote Ya Buɗe Wa Ƴan Nijeriya Ido – FCMB

September 19, 2026
Ku Bar Tinubu Ya Kammala Shekaru 8, Nigeria Forward Ta Nemi Ƴan Siyasar Arewa

Ku Bar Tinubu Ya Kammala Shekaru 8, Nigeria Forward Ta Nemi Ƴan Siyasar Arewa

September 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.