Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya ƙaddamar da zagaye na biyu na tarukan tattaunawa a matakin mazabu domin shirya kasafin kuɗin jihar na shekarar 2027, inda ya sake jaddada kudirin gwamnatinsa na tabbatar da shigar da al’umma cikin harkokin mulki.
Mai magana da yawun Gwamnan Jihar Katsina, Ibrahim Kaula Mohammed ne ya bayyana haka acikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar 18 ga watan Yuli, 2026.
Ya bayyana cewa, an ƙaddamar da shirin ne a Mazaɓar Radda da ke Ƙaramar Hukumar Charanchi, yayin da aka gudanar da irin wannan tattaunawa lokaci guda a dukkan mazabu 361 da ke ƙananan hukumomi 34 na jihar.Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Radda ya bayyana cewa tattaunawar ci gaba ce na alkawarin da gwamnatinsa ta ɗauka na sanya jama’a a cikin tsarin mulki. Ya ce kowace al’umma ta cancanci a saurare ta, kuma gudummawar mazauna jihar na da matuƙar muhimmanci wajen tsara manufofin gwamnati da kuma makomar ci gaban Jihar Katsina.
Gwamnan ya tuna cewa tattaunawar farko da aka gudanar kafin shirya kasafin kuɗin shekarar 2026 ta kafa tarihi, domin a karon farko al’ummar dukkan mazabu 361 sun samu damar ba da tasiri kai tsaye wajen tsara ayyukan gwamnati. Ya bayyana cewa da dama daga cikin shawarwarin da aka tattara a wancan lokaci sun zama ayyukan raya ƙasa da ake aiwatarwa a fannoni kamar gine-ginen tituna, lafiya, ilimi, noma, samar da ruwan sha, ƙarfafa matasa, walwalar jama’a, ci gaban al’umma da kuma tallafa wa harkokin tsaro.
Gwamna Radda ya amince cewa duk da ƙarancin albarkatun gwamnati, ba a yin watsi da buƙatun al’umma na gaskiya. Ya bayyana cewa duk shawarwarin da ba za a iya aiwatar da su nan take ba ana adana su domin la’akari da su a kasafin kuɗi na gaba ko wasu shirye-shiryen gwamnati. Haka kuma ya bukaci al’umma su riƙa sa ido kan yadda ake aiwatar da ayyuka domin ƙarfafa gaskiya, riƙon amana da kuma tabbatar da amfani mai kyau da kuɗaɗen jama’a.Ya kuma ƙarfafa gwiwar mazauna jihar da su shiga tattaunawar tare da gabatar da ayyuka masu ma’ana da za su magance manyan matsalolin al’ummominsu. Musamman ya yi kira ga matasa, mata, masu buƙata ta musamman, manoma, ‘yan kasuwa, masu sana’o’i da ƙungiyoyin al’umma da su yi amfani da wannan dama, yana mai jaddada cewa ci gaba mai ɗorewa ba zai samu ba sai da haɗin gwiwa tsakanin gwamnati da jama’a.
Tun da farko, Kwamishinan Kasafi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki, Alhaji Malik Anas, ya ce gwamnatin Radda ta kafa tarihi ta hanyar gudanar da tattaunawar kasafin kuɗi a dukkan mazabu 361 kafin kasafin kuɗin shekarar 2026. Ya tabbatar wa mahalarta taron cewa za a rubuta, a tantance tare da haɗa dukkan shawarwarin da aka samu cikin tsarin tsare-tsaren gwamnati gwargwadon albarkatun da ake da su da kuma abubuwan da gwamnati ta bai wa fifiko.
Ya kuma bukaci jama’a su mayar da hankali kan ayyuka masu amfani da za su inganta rayuwar al’umma.Shi ma Mai Kula da Shirin Ci Gaban Al’umma (CDP), Dakta Kamaludeen Kabir, ya sake jaddada cewa ci gaba mai ɗorewa ba zai tabbata ba sai idan al’umma da kansu sun gano abubuwan da suka fi buƙata kuma suka shiga cikin yanke shawarar da ta shafi rayuwarsu.
Ya bayyana cewa shirin CDP ya tura jami’ansa zuwa matakin ƙasa domin jagorantar tattaunawar, tattara buƙatun al’umma da tabbatar da cewa an haɗa dukkan shawarwarin da suka dace cikin shirye-shiryen kasafin kuɗin shekarar 2027.
An shirya tarukan ne ƙarƙashin jagorancin Ma’aikatar Kasafi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki tare da haɗin gwiwar Shirin Ci Gaban Al’umma (CDP) ƙarƙashin taken “Building Your Future IV.” Manufar shirin ita ce bai wa al’ummar dukkan mazabu 361 damar taka rawa kai tsaye wajen tsara kasafin kuɗin Jihar Katsina na shekarar 2027.
Taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, sarakunan gargajiya da na addini, wakilan al’umma da sauran masu ruwa da tsaki, lamarin da ya sake nuna kudirin gwamnatin Radda na tabbatar da shugabanci mai haɗa kowa da kowa, gaskiya, riƙon amana da ci gaban da jama’a ke jagoranta.














