Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, zai halarci zama na 81 na Babban Taron Majalisar Dinkin Duniya (UNGA) da za a gudanar a birnin New York a watan Satumba, inda ake sa ran zai gabatar da jawabi ga shugabannin ƙasashen duniya kan muhimman batutuwan da suka shafi Nijeriya da duniya baki ɗaya.
Jakadan dindindin na Nijeriya a Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD), Jimoh Ibrahim, ya bayyana cewa Shugaba Tinubu ya tabbatar da halartar taron bayan ya amince da shirye-shiryen da aka yi domin wakilcin Nijeriya a babban taron na bana.
A cewarsa, baya ga gabatar da jawabi a babban zauren Majalisar Ɗinkin Duniya, shugaban ƙasar zai kuma halarci wasu muhimman tarurrukan gefe da za su mayar da hankali kan batutuwan makamashi, ilimi da inganta harkokin kiwon lafiya. Haka kuma zai yi amfani da damar wajen bayyana sauye-sauyen tattalin arziki da na shugabanci da gwamnatin Nijeriya ke aiwatarwa.
Ambasada Ibrahim ya kuma ce Shugaba Tinubu zai tattauna da shugabannin duniya kan hanyoyin ƙarfafa tsaron iyakokin ƙasashen Yammacin Afirka domin magance matsalolin tsaro da ke ƙaruwa a yankin. Ya bayyana cewa Nijeriya ta fara aiki tare da MDD kan wani shiri na inganta tsaron iyakoki, kuma za ta nemi ƙarin goyon bayan ƙasashen duniya.
Shugaba Tinubu ya halarci zaman UNGA na 78 da kansa, yayin da Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya wakilce shi a zaman na 79 da na 80. Ana sa ran zama na 81 zai fara ne a ranar 8 ga Satumba, yayin da muhawarar shugabannin ƙasashe za ta gudana daga ranar 22 zuwa 28 ga Satumba, inda za a tattauna batutuwan sauyin yanayi, ci gaba mai ɗorewa, zaman lafiya, tsaro da sauran manyan ƙalubalen da duniya ke fuskanta.














