ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dambarwar Da Ta Biyo Bayan Sauya Sheƙar Gwamna Yusuf Na Jihar Kano

by Sulaiman
7 months ago
Kano

Batun sauya sheƙa daga wata jam’iyyar siyasa zuwa wata, wani alamari ne da yake da dogon tarihi a siyasar Nijeriya, tun daga jamhuriyar siyasa ta farko kamun akai ga samun ‘yancin-kai daga Turawan Mulkin Mallaka na Birtaniya.

 

Manyan ‘yan siyasa irin su marigayi Malam Aminu Kano da Malam Sa’adu Zungur da ire-irensu, jam’iyyar NPC suka fara yi farko, kafin su tattara kayansu zuwa jam’iyyar NEPU. A wannan zamani kuma, irin su jagoran Kwankwasiyya, Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso, sun yi sauye-sauye a tsakanin Jam’iyyun PDP, APC, da NNPP a yanzu.

ADVERTISEMENT
  • Muhimmanci Da Amfanin Shan Rake Ga Lafiyar Dan Adam
  • Hotuna: Babbar Mota Ta Hallaka Wata Bafulatana A Bauchi

Rikicin da ya dabaibaye batun sauya sheƙar gwamna Yusuf na jihar Kano daga Jam’iyyar NNPP zuwa APC, inda wasu ke ganin hakan butulci ne ga maigidansa Kwankwaso wasu kuma ke ganin hakan ba laifi ba ne, lissafin siyasa ne kawai.

 

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

A cewar masu ganin laifin gwamna Abba, suna nanata cewa, “tun da Kwankwaso ne silar Abba ya zama gwamnan Kano, lallai ne ya ci gaba da zama tare da shi a siyasance, da daɗi da ba daɗi.”

 

In ba a manta ba, A ranar Litinin, 26 ga Janairu, 2026, Gwamnan Jihar Kano ya sauya sheka zuwa Jam’iyyar APC, bayan ya sanar da yin murabus daga NNPP a ranar Juma’a, 23 ga Janairu, 2026, ƙasa da shekaru uku bayan lashe zaben gwamnan Kano.

 

Gwamnan ya ce rikicin cikin gida, rikicin shugabanci da shari’o’i a kotu, sun raunana jam’iyyar tare da raba kan mambobinta.

 

Ya ƙara da cewa, komawarsa APC za ta ba shi damar yin aiki kafaɗa-da-kafaɗa da Gwamnatin Tarayya domin kawo ayyukan raya ƙasa da ci gaban Kano.

 

Wannan na ɗauke ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya sanya hannu a ranar Juma’a.

 

Ya ce ya ɗauki matakin ne bayan dogon tunani, inda ya ce zai ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da zaman lafiya, haɗin kai da ci gaban Jihar Kano.

 

Sanarwar ta kuma bayyana cewa mambobi 21 na Majalisar Dokokin Jihar Kano, mambobi takwas na Majalisar Wakilai, da shugabannin ƙananan hukumomi 44 sun fice daga NNPP tare da gwamnan.

 

Duk da cewa, Gwamna Abba ya nannata cewa, ya yi shawarwari da na gabanshi a siyasa kafin sauya sheƙar amma abun mamaki sai ga maigidansa a siyasa, Jagoran Kwankwasiyya, Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso yana cewa, duk wanda ya yi masa butulci sai ya yi nadama.

 

“Ficewar Gwamna Abba daga NNPP ta zo wa mutane da yawa mamaki, ya ƙara da cewa shi ma da farko ya ji kamar mafarki ne,” in ji Kwankwaso.

 

Don haka, Kwankwaso ya bayyana ranar 23 Ga Janairu a matsayin Ranar Cin Amana ta Duniya.

 

Itama a nata ɓangaren, jam’iyyar NNPP cewa ta yi, sauya sheƙar Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir zuwa jam’iyyar APC cin amana ne ga jam’iyyar, jagoranta Sanata Rabiu Kwankwaso, da kuma al’ummar Kano.

 

Kakakin NNPP, Ladipo Johnson, ya ce jam’iyyar ba ta da ƙarfi sosai a Kano kafin zaɓen 2023, amma ta samu nasara ne saboda tasirin Kwankwaso da goyon bayan jama’a.

 

Jim kaɗan bayan sauya sheƙar gwamnan a hukumance wanda aka yi bikin murna a babban ɗakin taro na ‘Coronation Hall’ da ke gidan gwamnatin Kano, a yayin da yake jawabi, ɗaya daga cikin manyan baƙi, tsohon gwamnan Kano kuma tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya shaidawa gwamnan cewa, babu wanda zai yi takara da shi a zaɓen 2027 mai zuwa, inda shi ma, mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau Jibrin ya umurci duk mabiyan sa da su yi wa gwamna Abba mubaya’a.

 

Mataimakin gwamnan jihar Kano, Kwamared Abdulsalam Gwarzo, bai halarci taron sauya shekar maigidansa, gwamna Yusuf ba zuwa jam’iyyar APC, wanda hakan ke nuna gagarumin saɓani a siyasar jihar kafin babban zaɓen 2027.

 

Bayan haka, an samu rahotonnin wasu Kwamishinoni da masu riƙe da muƙaman siyasa duk sun yi murabus daga muƙamansu don nuna ɓacin ransu da kuma jaddada mubaya’arsu ga jagoran tafiyar aƙidar Kwankwasiyya, Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso.

Kano
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Shugaban Kasar Sin Ya Gana Da Firaministan Birtaniya 

Shugaban Kasar Sin Ya Gana Da Firaministan Birtaniya 

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.