Jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP) ta fara shigar da sunayen ’yan takararta domin zaɓen 2027, tare da neman Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta ƙara mata wa’adin kammala aikin.
Shugaban jam’iyyar na ƙasa, Dokta Agbo Major, ne, ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da aka gudanar a hedikwatar jam’iyyar da ke Abuja ranar Laraba.
Major ya ce jam’iyyar ta fara aikin ne bayan INEC ta ba ta izinin domin shigar da bayanan ’yan takara, amma lokaci ya yi mata kaɗan wajen kammala ɗora dukkanin takardu.
“Muna fuskantar ƙarancin lokaci. Mun roƙi INEC ta sake duba jadawalinta domin a samu adalci, don mu iya kammalawa tare da gabatar da ƙwararrun ’yan takara,” in ji shi.
Ya bayyana fara aikin shigar da sunayen ’yan takarar a matsayin babban mataki bayan watanni da jam’iyyar ta shafe tana fama da rikicin shugabanci.
Major ya kuma ce jam’iyyar ta dawo da kundin tsarin mulkinta na shekarar 2022 da kuma manufofinta, sannan za ta gudanar da babban taron kwamitin zartarwa na ƙasa (NEC) nan gaba domin amincewa da wasu muhimman shawarwari.
Ya gode wa shugabannin jam’iyyar, magoya bayanta da kuma ɓangaren shari’a bisa goyon bayan da suka bayar a lokacin da jam’iyyar ke fuskantar rikici, yana mai cewa NNPP a shirye take ta samar da ingantaccen shugabanci a zaɓen 2027.













