ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darussan Koyo Daga Salon Bunkasa Kasa Na JKS

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 days ago
Jks

Yayin da jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin ko JKS ke ciki shekaru 105 da kafuwa, masharhanta na ta bayyana ra’ayoyinsu dangane da gagarumar gudunmawa da jam’iyyar ta bayar a fannin bunkasa ci gaban kasar Sin, irin ci gaban da ya zamo mai matukar ban mamaki da kayatarwa.

Ko shakka babu JKS ta dora kasar Sin kan turbar ci gaba mai inganci, kuma mai dacewa da yanayin da kasar ke ciki, ta kuma samar da wani kyakkyawan misali na yadda kasashe daban daban, musamman masu tasowa za su iya zabar turbar ci gaba mafi dacewa da yanayin da suke ciki maimakon koyi ido rufe daga wasu sassa na daban. A kasar Sin JKS ta samar da nata manufofi masu nagarta, wadanda suka dace da yanayin kasar Sin, an kuma ci gaba da aiwatar da sauye-sauye kan tsare-tsaren wucin gadi, kafin aiwatar da manufofi masu game dukkanin kasa. Ta haka ne kuma kasar Sin ta kai ga kafa manyan tsare-tsaren raya kasa masu dacewa da al’ummunta.

Kamar yadda shaidun zahiri suka nuna, karkashin jagorancin JKS, kasar Sin ta yi nasarar bunkasa tattalin arziki, da daidaita yanayin zamantakewar al’ummun kasar yadda ya kamata. Inda a yanzu al’ummun kasar ke cin gajiyar nasarori masu dorewa.

ADVERTISEMENT

A bangaren zamanantar da kasa, baya ga samar da manufoin farfado da kasar Sin, JKS ta kuma jagoranci sabbin hanyoyi na ingiza ci gaba, irin wadanda tabbas sauran kasashe masu tasowa, kamar na Larabawa da na nahiyar Afirka za su iya koyi da su wajen cimma nasu nasarorin. A zahirin gaskiya, JKS ta wanzar da karsashi, da karbuwa tsakanin al’ummun kasar Sin, kuma dalilin hakan shi ne yadda ta mayar da burikan jama’a gaban komai. JKS ta jagoranci tsame kusan mutum miliyan 100 daga kangin matsanancin talauci, tare da kafa tsarin kiyaye walwalar jama’a mafi girma da nagarta a duniya.

Wasu karin fannoni da JKS ta yi fice sun hada da kyautata jagoranci, da karfafa da’a, da ingiza nagartar aiki, da yaki da cin hanci da rashawa, wasu dabi’u suka taimaka wajen inganta ikon jam’iyyar na samar da shugabanci na gari da karfafa gwiwar jami’ai a dukkanin matakai.

LABARAI MASU NASABA

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Yayin da kasar Sin ke kara samun ci gaba karkashin jagorancin JKS, tana kuma karfafa hadin gwiwa da sauran sassa, bisa kudurorin hadin kai daban daban, irin su dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka, da shawarar ziri daya da hanya daya da sauransu, wadanda kawo yanzu ke ta haifar da gajiya ta fannin samar da ababen more rayuwa, da makamashi da sauran muhimman fannoni.

Bahaushe kan ce, “Yabon gwani ya zama dole”, JKS ta yi an gani… kuma kwarewa, da gogewarta wajen samar da jagoranci mai nagarta da dorewa, ya zamo kyakkyawan abun koyi ga dukkanin kasashen duniya musamman masu tasowa, wadanda ke fatan saita akalar neman nasara bisa hakikanin halin da suke ciki. (Saminu Alhassan)

Jks
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Soki Abin Da Amurka Da Tarayyar Turai Ke Kira Da Wai ‘Damuwa Kan Sabuwar Dokar Kabilu’
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    CGTN Ta Gudanar Da Nazari Kan Yadda Jama’Ar Duniya Ke Kallon Amurka
Jks
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola
  • Sulaiman
    Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran
  • Sulaiman
    Sin Ta Soki Abin Da Amurka Da Tarayyar Turai Ke Kira Da Wai ‘Damuwa Kan Sabuwar Dokar Kabilu’
  • Sulaiman
    CGTN Ta Gudanar Da Nazari Kan Yadda Jama’Ar Duniya Ke Kallon Amurka

MASU ALAKA

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola
Daga Birnin Sin

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran
Daga Birnin Sin

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Sin Ta Soki Abin Da Amurka Da Tarayyar Turai Ke Kira Da Wai ‘Damuwa Kan Sabuwar Dokar Kabilu’
Daga Birnin Sin

Sin Ta Soki Abin Da Amurka Da Tarayyar Turai Ke Kira Da Wai ‘Damuwa Kan Sabuwar Dokar Kabilu’

July 3, 2026
Next Post
Binciken Ra’ayin Jama’a Na Duniya: Jam’iyyar Kwaminis Ta Sin Jagora Ce Mai Karfi

Binciken Ra'ayin Jama'a Na Duniya: Jam'iyyar Kwaminis Ta Sin Jagora Ce Mai Karfi

LABARAI MASU NASABA

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026
Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

July 4, 2026
Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.