Yayin da jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin ko JKS ke ciki shekaru 105 da kafuwa, masharhanta na ta bayyana ra’ayoyinsu dangane da gagarumar gudunmawa da jam’iyyar ta bayar a fannin bunkasa ci gaban kasar Sin, irin ci gaban da ya zamo mai matukar ban mamaki da kayatarwa.
Ko shakka babu JKS ta dora kasar Sin kan turbar ci gaba mai inganci, kuma mai dacewa da yanayin da kasar ke ciki, ta kuma samar da wani kyakkyawan misali na yadda kasashe daban daban, musamman masu tasowa za su iya zabar turbar ci gaba mafi dacewa da yanayin da suke ciki maimakon koyi ido rufe daga wasu sassa na daban. A kasar Sin JKS ta samar da nata manufofi masu nagarta, wadanda suka dace da yanayin kasar Sin, an kuma ci gaba da aiwatar da sauye-sauye kan tsare-tsaren wucin gadi, kafin aiwatar da manufofi masu game dukkanin kasa. Ta haka ne kuma kasar Sin ta kai ga kafa manyan tsare-tsaren raya kasa masu dacewa da al’ummunta.
Kamar yadda shaidun zahiri suka nuna, karkashin jagorancin JKS, kasar Sin ta yi nasarar bunkasa tattalin arziki, da daidaita yanayin zamantakewar al’ummun kasar yadda ya kamata. Inda a yanzu al’ummun kasar ke cin gajiyar nasarori masu dorewa.
A bangaren zamanantar da kasa, baya ga samar da manufoin farfado da kasar Sin, JKS ta kuma jagoranci sabbin hanyoyi na ingiza ci gaba, irin wadanda tabbas sauran kasashe masu tasowa, kamar na Larabawa da na nahiyar Afirka za su iya koyi da su wajen cimma nasu nasarorin. A zahirin gaskiya, JKS ta wanzar da karsashi, da karbuwa tsakanin al’ummun kasar Sin, kuma dalilin hakan shi ne yadda ta mayar da burikan jama’a gaban komai. JKS ta jagoranci tsame kusan mutum miliyan 100 daga kangin matsanancin talauci, tare da kafa tsarin kiyaye walwalar jama’a mafi girma da nagarta a duniya.
Wasu karin fannoni da JKS ta yi fice sun hada da kyautata jagoranci, da karfafa da’a, da ingiza nagartar aiki, da yaki da cin hanci da rashawa, wasu dabi’u suka taimaka wajen inganta ikon jam’iyyar na samar da shugabanci na gari da karfafa gwiwar jami’ai a dukkanin matakai.
Yayin da kasar Sin ke kara samun ci gaba karkashin jagorancin JKS, tana kuma karfafa hadin gwiwa da sauran sassa, bisa kudurorin hadin kai daban daban, irin su dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka, da shawarar ziri daya da hanya daya da sauransu, wadanda kawo yanzu ke ta haifar da gajiya ta fannin samar da ababen more rayuwa, da makamashi da sauran muhimman fannoni.
Bahaushe kan ce, “Yabon gwani ya zama dole”, JKS ta yi an gani… kuma kwarewa, da gogewarta wajen samar da jagoranci mai nagarta da dorewa, ya zamo kyakkyawan abun koyi ga dukkanin kasashen duniya musamman masu tasowa, wadanda ke fatan saita akalar neman nasara bisa hakikanin halin da suke ciki. (Saminu Alhassan)














