ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darussan Koyo Daga Salon Bunkasa Kasa Na JKS

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 weeks ago
Jks

Yayin da jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin ko JKS ke ciki shekaru 105 da kafuwa, masharhanta na ta bayyana ra’ayoyinsu dangane da gagarumar gudunmawa da jam’iyyar ta bayar a fannin bunkasa ci gaban kasar Sin, irin ci gaban da ya zamo mai matukar ban mamaki da kayatarwa.

Ko shakka babu JKS ta dora kasar Sin kan turbar ci gaba mai inganci, kuma mai dacewa da yanayin da kasar ke ciki, ta kuma samar da wani kyakkyawan misali na yadda kasashe daban daban, musamman masu tasowa za su iya zabar turbar ci gaba mafi dacewa da yanayin da suke ciki maimakon koyi ido rufe daga wasu sassa na daban. A kasar Sin JKS ta samar da nata manufofi masu nagarta, wadanda suka dace da yanayin kasar Sin, an kuma ci gaba da aiwatar da sauye-sauye kan tsare-tsaren wucin gadi, kafin aiwatar da manufofi masu game dukkanin kasa. Ta haka ne kuma kasar Sin ta kai ga kafa manyan tsare-tsaren raya kasa masu dacewa da al’ummunta.

Kamar yadda shaidun zahiri suka nuna, karkashin jagorancin JKS, kasar Sin ta yi nasarar bunkasa tattalin arziki, da daidaita yanayin zamantakewar al’ummun kasar yadda ya kamata. Inda a yanzu al’ummun kasar ke cin gajiyar nasarori masu dorewa.

ADVERTISEMENT

A bangaren zamanantar da kasa, baya ga samar da manufoin farfado da kasar Sin, JKS ta kuma jagoranci sabbin hanyoyi na ingiza ci gaba, irin wadanda tabbas sauran kasashe masu tasowa, kamar na Larabawa da na nahiyar Afirka za su iya koyi da su wajen cimma nasu nasarorin. A zahirin gaskiya, JKS ta wanzar da karsashi, da karbuwa tsakanin al’ummun kasar Sin, kuma dalilin hakan shi ne yadda ta mayar da burikan jama’a gaban komai. JKS ta jagoranci tsame kusan mutum miliyan 100 daga kangin matsanancin talauci, tare da kafa tsarin kiyaye walwalar jama’a mafi girma da nagarta a duniya.

Wasu karin fannoni da JKS ta yi fice sun hada da kyautata jagoranci, da karfafa da’a, da ingiza nagartar aiki, da yaki da cin hanci da rashawa, wasu dabi’u suka taimaka wajen inganta ikon jam’iyyar na samar da shugabanci na gari da karfafa gwiwar jami’ai a dukkanin matakai.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

Yayin da kasar Sin ke kara samun ci gaba karkashin jagorancin JKS, tana kuma karfafa hadin gwiwa da sauran sassa, bisa kudurorin hadin kai daban daban, irin su dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka, da shawarar ziri daya da hanya daya da sauransu, wadanda kawo yanzu ke ta haifar da gajiya ta fannin samar da ababen more rayuwa, da makamashi da sauran muhimman fannoni.

Bahaushe kan ce, “Yabon gwani ya zama dole”, JKS ta yi an gani… kuma kwarewa, da gogewarta wajen samar da jagoranci mai nagarta da dorewa, ya zamo kyakkyawan abun koyi ga dukkanin kasashen duniya musamman masu tasowa, wadanda ke fatan saita akalar neman nasara bisa hakikanin halin da suke ciki. (Saminu Alhassan)

Jks
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi
Jks
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya
  • Sulaiman
    Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya
  • Sulaiman
    Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150
  • Sulaiman
    Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

MASU ALAKA

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150
Daga Birnin Sin

Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

July 24, 2026
Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba

July 23, 2026
Next Post
Binciken Ra’ayin Jama’a Na Duniya: Jam’iyyar Kwaminis Ta Sin Jagora Ce Mai Karfi

Binciken Ra'ayin Jama'a Na Duniya: Jam'iyyar Kwaminis Ta Sin Jagora Ce Mai Karfi

LABARAI MASU NASABA

NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

July 24, 2026
Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026
NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

July 24, 2026
Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

July 24, 2026
Kwairanga Ya Kafa Tarihi A Shugabancin Hukumar Kula Da Kasuwar Hannun Jari Ta Nijeriya

Kwairanga Ya Kafa Tarihi A Shugabancin Hukumar Kula Da Kasuwar Hannun Jari Ta Nijeriya

July 24, 2026
Yadda Kotun Daukaka Kara Ta Kama Hanyar Cin Gashin Kanta

Yadda Kotun Daukaka Kara Ta Kama Hanyar Cin Gashin Kanta

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.