ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kotun Daukaka Kara Ta Kama Hanyar Cin Gashin Kanta

by Shuaibu Shuaibu
41 minutes ago
Kotun

Baya ga sakamakon shari’o’in zaben shugaban kasa da gwamnonin jihohi, wanda kotun koli za ta yanke hukunci na karshe, alkaliyar kotun daukaka kara, Monica Dongban-Mensem, za ta zama jami’ar shari’a mafi tasiri a zaben 2027.

Dongban-Mensem tana da damar tantance makomar siyasa ta ‘yan takarar majalisa a cikin daruruwan kalubalen shari’a da ka iya zuwa kafin da bayan zabukan.

Shugabar kotun daukaka kara na iya jagorantar kotun sauraron karar zaben shugaban kasa da kanta kuma watakila ta kafa ma’aunin shari’a wajen tantance sakamakon zabe, wanda zai tilasta alkalan kotun koli bin wannan ma’auni nata.

ADVERTISEMENT

A matsayin shugabar kotun daukaka kara, za ta zabi alkalan wadanda za su jagoranci shari’a a kotun sauraron karar zabe a jihohi 36 da Abuja don yanke hukunci kan wadanda suka samu rasara da kuma wadanda suka sha kaye.

Alkalan da ta zaba su jagoranci shari’ar kotun sauraron karar zabe mai yuwuwa za su nuna kimominta, kuma hukuncin da suka yanke na iya tasiri a dimokuradiyyar Nijeriya da rawar da kotun ke takawa wajen fassara dokokin zabe.

LABARAI MASU NASABA

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Haka kuma, a matsayinta ta shugabar kotun daukaka kara, Ayo Salami ya jagoranci kotunan sauraron karar zabe da suka sake rubuta dokokin ‘yanci da rarrabuwa ikon, kuma suka rage karfin jam’iyya mai mulki a jihohi.

Rashin nasarar da PDP ta sha tsawon shekaru da dama, daga 2007 zuwa 2010, sun sa majalisar kasa ta yi gyara a dokar zabe don ba kotun kolin iko na karshe a rikice-rikicen zabe da suka shafi zaben gwamnoni.

Yayin da wasu masana ke ganin raba gidaje ga alkalai na kotun daukaka kara Abuja a matsayin wata boyayyiyar hanya ta samun goyon bayan kotuna, sai dai babu wata alama da ke nuna hakan na faruwa.

Daga sabbin hukuncin da bangarori daban-daban suka yanke, Dongban-Mensem, tana tafiyar da harkokinta cikin tsari ba tare da katsalandan ba, sai dai watakila ra’ayinta ne kawai game da yadda ta dauki dokar shari’a a Nijeriya.

A Zahiri kotun daukaka kara tana aiki da ‘yancin kanta tun daga kananan kotuna zuwa kotun koli ta kasa da tasirin sauran rassan gwamnati guda biyu.

A watan Yuni, wata kotu ta umarci dakatar da aiwatar da hukuncin babbar kotun tarayya wanda ya tilasta wa INEC cire rajistar jam’iyyun siyasa guda biyar na adawa, ciki har da ADC.

A cikin hukuncin kotu na kwanan nan, tsarin kwamitin mutane uku da ke yanke hukunci ya bayyana komai da ake bukata a sani game da siyasar Dongban-Mensem.

Idan ka kalle su sosai, alkalin da suka zauna a kwamitocin su kansu suna nuna a wane bangare kotu za ta karkata. Kuma kamar Ayo Salami, zabin da take yi na iya gina ko rushe jam’iyyun siyasa ko canza tafarkin dimokuradiyyar Nijeriya.

Kotun
Shuaibu Shuaibu
+ postsBio
  • Shuaibu Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/shuaibu-shuaibu/
    Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka
  • Shuaibu Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/shuaibu-shuaibu/
    Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba
  • Shuaibu Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/shuaibu-shuaibu/
    Ibrahim Aliyu Na Ci Gaba Da Rasa Tasiri A Harkar Fili Da Gidaje A Yankin Abuja
  • Shuaibu Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/shuaibu-shuaibu/
    Fafutukar Neman Sabon Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya

MASU ALAKA

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka
Bakon Marubuci

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba
Bakon Marubuci

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki
Bakon Marubuci

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki

June 12, 2026

LABARAI MASU NASABA

Yadda Kotun Daukaka Kara Ta Kama Hanyar Cin Gashin Kanta

Yadda Kotun Daukaka Kara Ta Kama Hanyar Cin Gashin Kanta

July 24, 2026
Yadda ‘Yan Spain Suka Mamaye Kyaututtukan Kofin Duniya

Yadda ‘Yan Spain Suka Mamaye Kyaututtukan Kofin Duniya

July 24, 2026
Kotun

Wasiƙar Trump Ba Za Ta Ceto Tinubu Daga Faduwa Zaɓe Ba – Jam’iyyar ADC

July 24, 2026
Falalar Yawaita Istigifari (2)

Falalar Yawaita Istigifari (2)

July 24, 2026
Kotun

Amurka Ta Kakaba Harajin Kaso 12.5% A Kan kayayyakin Nijeriya

July 24, 2026
Wane Ne Gwarzo Tsakanin Pele Da Maradona Da Messi?

Wane Ne Gwarzo Tsakanin Pele Da Maradona Da Messi?

July 24, 2026
Nijeriya Ta Tabka Asarar Naira Biliyan 2.61 A Samar Da Wuta A Zangon Farko Na 2026 —NERC

Nijeriya Ta Tabka Asarar Naira Biliyan 2.61 A Samar Da Wuta A Zangon Farko Na 2026 —NERC

July 24, 2026
NPA Ta Goyi Bayan Yarjejeniyar Shirin Bayar Da Horo Na Musamman Domin Tafiyar Da Tashoshin Jiragen Ruwa

NPA Ta Goyi Bayan Yarjejeniyar Shirin Bayar Da Horo Na Musamman Domin Tafiyar Da Tashoshin Jiragen Ruwa

July 24, 2026
Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

July 24, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.