Kwanan nan, mutane 11,521 daga kasashe 41 na duniya sun bayyana ra’ayoyinsu a wani binciken jin ra’ayin jama’a da ya shaida kasancewar “Jam’iyyar kwaminis ta Sin ko JKS jagora mai karfi” wadda kuma ta yi matukar burge su.
A bangaren ayyukan mulki, kaso 57.4% na masu bayyana ra’ayoyin daga kasashe masu tasowa sun darajanta ingancin jagorancin JKS. Daga cikinsu, ’yan kasashe kamar Najeriya, da Pakistan, da Vietnam da sauransu sun yi matukar jinjinawa ayyukan mulki na JKS, inda mizanin yardarsu da jam’iyyar ya zarce kaso 70%.
Masu bayyana ra’ayoyin sun kuma nuna cewa, fannoni uku da JKS ta fi taka rawa a ayyukan mulki, su ne “inganta ababen more rayuwa”, da “inganta ilimi” da kuma “samar da ayyukan yi”.
Wannan bincike na jin ra’ayin jama’a, wanda sashin CGTN na babban rukunin gidan radiyo da talabijin na kasar Sin CMG, tare da jami’ar jama’ar ta kasar Sin suka gudanar, ya gudana ne karkashin kwalejin binciken harkokin watsa labarai a sabon zamani. (Amina Xu)














