Kungiyar masana’antun auduga ta kasar Sin ta kalubalanci matakin Amurka na baya-bayan nan, na sanya karin kamfanonin kasar Sin 43, ciki har da kamfanonin sarrafa auduga, cikin jadawalin da ta kira na “Dokar dakile kwadagon tilas na ’yan Uyghur”.
An shafe shekaru da dama, Amurka tana sake sabunta matakanta na fakewa da batun hakkin dan Adam wajen kakaba wa kamfanonin Sin takunkumai, tana cewa ana tilastawa ’yan kabilar Ugyur kwadago.
Amma abun tambaya a nan shi ne, shin Amurka tana da kwararan shaidu dake tabbatar da hakan? Shin takunkuman da take kakaba wa na dogaro ne da sabbin shaidun da take samu ko kuwa? Ko bambancin ra’ayi kan tsarin tafiyar da harkokin kasa ya zama laifi? A wannan zamani da Sin ke kan gaba wajen kirkirowa da amfani da fasahohi da kayayyakin aiki na zamani a duniya, me zai sa ta nace wajen tilasta kwadago bayan tana da karfin samar da kayayyakin da za su iya rubanya kokarin dan adam fiye da sau 10? Abun da zai bayar da mamaki shi ne, ko a da can da aka fi amfani da jama’a wajen aiwatar da ayyuka, mutane da dama daga sassan kasar Sin ne ke zuwa jihar Xinjiang a lokacin girbin auduga domin shiga aikin don samun kudin shiga. Yayin wata ziyarar da na yi a jihar, na samu damar tattauna da wasu mutane da suka shaida min bisa radin kansu cewa, asalinsu ba ’yan jihar ba ne, kuma aikin girbin auduga ne ya sa iyayensu kaura zuwa jihar Xinjiang.
To su da suka fito daga sauran sassan kasar Sin, tilasta musu aka yi?Ya kamata masu neman dakile ci gaban Sin ko son dusashe haskenta su fahimci cewa, hakar su ba za ta cimma ruwa ba, domin kasar Sin na fadada bude kofarta ga kasa da kasa.
Kuma a yanzu duniya tana tafin hannun jama’a. Kafafen yada labarai masu tsare gaskiya da kafofin sada zumunta na kara wayar da kan al’umma game da ainihin yanayin da ake ciki, kuma za su iya bambance gaskiya da akasinta. (Faeza Mustapha)














