ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dole A Hukunta Wadanda Suka Kai Harin Bom A Kaduna -Majalisar Dattawa

by Sulaiman
3 years ago
majalisar kasa

Majalisar Dattawan Nijeriya ta lashi takobin gudanar da bincike kan harin kuskuren da rundunar sojin kasar ta kai, da ya janyo mutuwar mutane da dama a Jihar Kaduna.

Kawo yanzu dai mutane da dama ne suka rasa rayukansu ba, yayin da kuma wasu ke kwance a gadon asibiti ana kula da lafiyarsu.

  • Yawan Yaran Da Ke Fama Da Cututtuka Masu Alaka Da Sassan Jiki Masu Taimakawa Numfashi Ya Ragu A Kasar Sin
  • Tinubu Zai Sake Fuskantar Wata Shari’ar A Kotun Koli Kan Zaben 2023

Sanata Lawal Adamu Usman, (Mr La), shi ne dan majalisar dattawan Nijeriya mai wakiltar Kaduna ta tsakiya, inda aka kai harin, ya shaida wa BBC cewa al’amari ne da ba za su bari ya wuce ba:

ADVERTISEMENT

“Wannan abu ne da ba za mu bari ya wuce ba, za mu sa a bincika a gano dalilin da ya sa ake samun irin wannan iftila’i. Mutane na yin ibadarsu a zo a jefa mu su bam, sai mun binciko abin da ya faru kuma a dauki mataki akan wadanda suka kai harin” in ji shi.

Gomman mutane ake fargabar sun rasa rayukansu bayan harin bam da jirgin saman yakin ya kai wa gungun masu Mauludi bisa kuskure a kauyen Tudun Biri da ke Karamar Hukumar Igabi .

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

Sai dai duk da cewa yanki ne da ke fama tashin hankali sakamakon hare-haren ‘yan bindiga amma majalisar dattawan Nijeriya ta danganta al’amarin kan gazawar sojojin kasar wajen tattara bayanan sirri kamar yadda sanata Lawal Adamu Usman ya ce:

“Akwai gazawa wajen tattara bayanan sirri saboda ba bu yadda za a yi ka saki harsashi idan baka tabbatar da wurin da za ka kai harin ba ballantana bam.

Bam babban abu ne kafin a sake shi dole sai an tabbatar da cewa masu garkuwa da mutane ne a wurin. Kuma idan har akwai sakaci to za mu tabbatar cewa an kama mutanen kuma za’a hukuntansu “, in ji shi.

Tun farko Gwmnatin Jihar Kaduna ta kafa kwamitin bincike da aka dorawa alhakin gano abin da ya faru.

Ita ma majalisar dattawan kasar ta ce za ta kafa kwamitin binciken akan alamarin tare da kai dauki ga mutanen da alamarin ya rutsa da su.

Majalisar Dattawa
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Next Post
Adadin Hatsin Da Aka Girbe A Sin A Bana Ya Kai Matsayin Koli

Adadin Hatsin Da Aka Girbe A Sin A Bana Ya Kai Matsayin Koli

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.