Babban Jami’in Da’awa na ƙungiyar Nasrul-Lahi-l-Fatih Society (NASFAT), Abdul-Ganiyy Raji, ya bayyana cewa ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga da ke addabar Nijeriya ba Musulmi ba ne kuma ba sa wakiltar koyarwar addinin Musulunci, yana mai jaddada cewa Musulunci addini ne na zaman lafiya, haƙuri da zaman tare cikin lumana.
Raji ya bayyana hakan ne ranar Laraba yayin wata hira a shirin ‘Morning Brief’ na gidan talabijin na Channels, yayin da Musulmi a faɗin ƙasar ke gudanar da bikin Eidin layya.
Da yake mayar da martani kan matsalolin ta’addanci da ayyukan ‘yan bindiga da ake dangantawa da ƙungiyoyin masu tsattsauran ra’ayi kamar Boko Haram, malamin NASFAT ya ce shugabannin Musulmi sun sha yin Allah-wadai da ta’addanci da tashin hankali, sabanin zargin da ake yi cewa malamai sun yi shiru.
“Malamai da dama sun fito sun bayyana cewa waɗannan mutane ba Musulmai ba ne. Waɗannan mutane ba Musulmai ba ne,” in ji shi.
“Kuma zan sake faɗa a nan cewa ba sa wakiltar Musulunci.”















Discussion about this post