An gudanar da zangon farko na bikin tallata fina-finan kasar Sin mai suna “Reel China”, a gidan sinima na Nu Metro dake babban kantin Hyde Park dake birnin Johannesburg na kasar Afirka ta Kudu, a jiya Talata 26 ga watan nan, inda jakadan Sin da ke Afirka ta Kudu, Wu Peng, da jami’an ma’aikatar harkokin wajen Afirka ta Kudu, da wakilai daga bangarorin al’adu, da kafafen yada labarai, da matasan dalibai, da Sinawa dake zaune a kasar sama da dari suka halarci bikin.
Bikin ya samu goyon-baya daga hukumar kula da fina-finai ta kasar Sin, wanda babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin wato CMG a takaice ya dauki nauyin shiryawa, kuma bikin daya ne daga cikin muhimman bukukuwan musanyar al’adu, karkashin taken “shekarar musanyar al’adu da cudanyar jama’a tsakanin Sin da Afirka” ta 2026.A jawabinsa, jakada Wu Peng ya bayyana cewa, babban tushen dangantakar Sin da Afirka shi ne jama’a, kuma musanyar fina-finai da shirye-shiryen talabijin, wata muhimmiyar gada ce ta kara samun fahimtar juna tsakanin al’ummun bangarorin biyu.
A bana ake cika shekaru 70 da kaddamar da huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Afirka, kuma shekara ce ta musanyar al’adu, da cudanyar jama’a da bangarorin biyu suka ayyana tare. Bikin gabatar da fina-finan kasar Sin a kasashen waje na “Reel China”, wani muhimmin kokari ne da ake yi na tabbatar da matsayar da shugabannin Sin da na kasashen Afirka suka cimma, gami da zurfafa mu’amalar Sin da Afirka ta Kudu a bangaren al’adu da jama’a. (Murtala Zhang)















Discussion about this post