ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fafutukar Neman Sabon Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya

by Abubakar Sulaiman
11 seconds ago

Akwai babbar damar cewa mace ce za ta zama Babbar Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya na gaba. Haka kuma, akwai babbar damar cewa aikin Majalisar Ɗinkin Duniya zai je yankin Kudancin Amurka, idan aƙalla ƴan takarar guda da biyar suka fito daga wannan yanki.

Amma, hakan bai hana yiwuwar cewa wani daga wajen waɗannan rukuni biyu zai iya samun takara kuma a zaɓe shi daga ƙasashe fiye da 190 da ke cikin mambobin ƙungiyar.

Burundi ta zaɓi Macky Sall, tsohon shugaban ƙasar Senegal. Argentine ta zaɓi ɗan ƙasarta, Rafael Grossi, wanda shi ne shugaban IAEA.

ADVERTISEMENT

Sauran ƴan takara su ne, Michelle Jeria, tsohuwar shugabar Chile wacce ƙasashe uku suka zaɓe ta, da Rebeca Mayufis, tsohuwar mataimakiyar shugabar Costa Rica kuma a yanzu sakatariyar janar ta taron Majalisar Ɗinkin Duniya kan bunƙasa harkokin kasuwanci.

A kwanan nan, Maria Espinosa Garces, wacce ta riƙe muƙamin ministan harkokin wajen Ecuador sau biyu kuma ta riƙe muƙamin ministan tsaro da wakilar Guyana a Majalisar Ɗinkin Duniya, Carolyn Brikett, sun samu zaɓi daga ƙasashensu na asali.

LABARAI MASU NASABA

NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

“Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

A matsayin wani ɓangare na tsarin zaɓen, duk sun yi zaman tattaunawa da ƙasashe mambobi da ƙungiyoyin farafen huɗa domin tallata manufofinsu idan aka zaɓe su.

Sai dai Shugaban Majalisar Ɗinkin Duniya na yanzu ya buƙaci ƙasashen su zaɓi ƙarin ƴan takara don maye gurbin Sakataren Janar António Guterres, wanda wa’adinsa zai ƙare a watan Janairu 2027.

Akwai wasu jerin sunayen jakadun da wasu shugabannin ƙasa mata da ake zargin za su iya maye gurɓinsa, amma ba a zaɓe su a hukumance ba. Wataƙila mafi shahara ita ce Jacinda Ardern, tsohuwar Firayim Minista ta New Zealand. A cikin wannan jerin sunayen da ake hasashe akwai Kristalina Georgieɓa, shugaban gudanarwa na IMF na yanzu. Har da Keir Starmer, tsohon Firayim Minista na Birtaniya, su shiga jerin sunayen.

Sannan akwai Amina Mohammed ta Nijeriya, Mataimakiyar Sakatariya Janar ta Majalisar Ɗinkin Duniya kuma shugabar rukunin ci gaban ɗorewar Majalisar Ɗinkin Duniya.

Tun daga 2012, tana da dogon tarihi na aiki tare da shawartar Majalisar Ɗinkin Duniya kan batutuwan ci gaba mai ɗorewa. Wannan ya faru tun kafin Gueterez ya naɗa ta a matsayin mataimakiyar sakatare janar.

A ƙarƙashin jagorancin Ban Ki-moon, Amina ta jagoranci tsarin da ya kai ga yarjejeniya ta duniya kan manufar ci gaba mai ɗorewa ta 2030 da manufofin samar da ci gaban ɗorewa.

A lokacin da yate Nijeriya, Amina ta yi aiki tare da shugabannin ƙasa huɗu a jere, da suka haɗa da Olusegun Obasanjo, wanda ta taimaka masa wajen rage bashi da suka kai kusan kasafin kuɗi na shekara-shekara na dala miliyan 100, zuwa Muhammadu Buhari, wanda ta yi aiki tare da shi a matsayin ministan muhalli.

A wani lokaci a aikinta, ta burge Bill Gates, wanda ya kafa Microsoft. Ita tana matuƙar so bunƙasa kafofin watsa labarai na Yamma. Amma a zahiri, ma’aikatar harkokin wajen Nijeriya ba su burge ta ba.

Sannan kuma Shugaba Bola Tinubu bai ga dalilin haɓaka martabarta ba a idon duniya ta hanyar zaɓen ta a kan muƙamin shugabar Majalisar Ɗinkin Duniya, ko da kuwa za a ɗaga matsayin Nijeriya a idon duniya.

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness
  • Abubakar Sulaiman
    NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN
  • Abubakar Sulaiman
    Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisar Kan Gyaran Kudirin Dokar Shari’ar Manyan Laifuka
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

MASU ALAKA

NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN
Labarai

NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Labarai

“Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

July 10, 2026
Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
Labarai

Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

July 10, 2026

LABARAI MASU NASABA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Fafutukar Neman Sabon Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

July 10, 2026
NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

“Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

July 10, 2026
Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

July 10, 2026
Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu

Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu

July 10, 2026
Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisar Kan Gyaran Kudirin Dokar Shari’ar Manyan Laifuka

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisar Kan Gyaran Kudirin Dokar Shari’ar Manyan Laifuka

July 10, 2026
Taƙaddamar Kafa Hukumar Bogi: Tinubu Ya Umarci A Yi Binciken Ƙwaƙwaf

Taƙaddamar Kafa Hukumar Bogi: Tinubu Ya Umarci A Yi Binciken Ƙwaƙwaf

July 10, 2026
Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

July 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.