Gwamnatin Jihar Kaduna ta yabawa Ofishin Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Harkokin Tsaro (ONSA) bisa ƙaddamar da shirin Forest Guards, tana mai bayyana shi a matsayin muhimmin mataki wajen magance matsalar rashin tsaro a dazuka da yankunan karkara. Gwamna Uba Sani ya bayyana hakan ne ranar Laraba yayin da ya karɓi wata babbar tawaga daga ONSA ƙarƙashin jagorancin Daraktan Harkokin Tsaro, Manjo Janar HI Mabeokwu, a Gidan Gwamnatin Kaduna.
Tawagar ta kai ziyarar ne domin tantance ci gaban horon sama da masu gadin daji 1,000 masu ɗauke da makamai, waɗanda ake shiryawa domin tura su zuwa yankunan da ake fama da matsalar tsaro a faɗin jihar Kaduna. Gwamna Uba Sani ya ce wannan shiri na nuna ƙudirin gwamnatin tarayya na ƙarfafa tsaro ta hanyar haɗin gwiwa da gwamnatocin jihohi, tare da tabbatar da cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da kula da jin daɗin masu horo da masu horas da su.
A nata ɓangaren, tawagar ONSA ta nuna gamsuwa da yadda horon ke gudana, tana mai cewa an tsara shirin cikin tsari kuma an samar da isassun kayan aiki da wuraren gudanar da horon. Har ila yau, ta yabawa gwamnatin Kaduna bisa tallafin jin daɗi da take bai wa masu horo da masu horas da su tun bayan fara shirin.
Jami’an da ke kula da shirin sun bayyana cewa masu horon sun kammala kusan kashi 60 cikin 100 na tsarin horaswar, wanda ya haɗa da koyon amfani da makamai, da dabarun gudanar da ayyukan tsaro da sauran ƙwarewar da ake buƙata wajen tsaron dazuka. Tawagar tantancewar ta ƙunshi wakilai daga Hukumar Leken Asiri ta Ƙasa (NIA), da Hukumar DSS, da kula da Gandun Daji, da Rundunar ‘Yansandan da kuma Sojojin Nijeriya. Shirin na daga cikin Presidential Forest Guards Initiative, wanda ke da nufin ƙwato dazukan da ‘yan ta’adda, da ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane ke amfani da su a matsayin mafaka, inda ake sa ran masu gadin dajin za su yi aiki tare da hukumomin tsaro wajen tattara bayanan sirri da sintiri a yankunan dazuka.













