ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

by Abubakar Sulaiman
58 minutes ago
Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Gwamnatin Jihar Kaduna ta yabawa Ofishin Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Harkokin Tsaro (ONSA) bisa ƙaddamar da shirin Forest Guards, tana mai bayyana shi a matsayin muhimmin mataki wajen magance matsalar rashin tsaro a dazuka da yankunan karkara. Gwamna Uba Sani ya bayyana hakan ne ranar Laraba yayin da ya karɓi wata babbar tawaga daga ONSA ƙarƙashin jagorancin Daraktan Harkokin Tsaro, Manjo Janar HI Mabeokwu, a Gidan Gwamnatin Kaduna.

Tawagar ta kai ziyarar ne domin tantance ci gaban horon sama da masu gadin daji 1,000 masu ɗauke da makamai, waɗanda ake shiryawa domin tura su zuwa yankunan da ake fama da matsalar tsaro a faɗin jihar Kaduna. Gwamna Uba Sani ya ce wannan shiri na nuna ƙudirin gwamnatin tarayya na ƙarfafa tsaro ta hanyar haɗin gwiwa da gwamnatocin jihohi, tare da tabbatar da cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da kula da jin daɗin masu horo da masu horas da su.

A nata ɓangaren, tawagar ONSA ta nuna gamsuwa da yadda horon ke gudana, tana mai cewa an tsara shirin cikin tsari kuma an samar da isassun kayan aiki da wuraren gudanar da horon. Har ila yau, ta yabawa gwamnatin Kaduna bisa tallafin jin daɗi da take bai wa masu horo da masu horas da su tun bayan fara shirin.

ADVERTISEMENT

Jami’an da ke kula da shirin sun bayyana cewa masu horon sun kammala kusan kashi 60 cikin 100 na tsarin horaswar, wanda ya haɗa da koyon amfani da makamai, da dabarun gudanar da ayyukan tsaro da sauran ƙwarewar da ake buƙata wajen tsaron dazuka. Tawagar tantancewar ta ƙunshi wakilai daga Hukumar Leken Asiri ta Ƙasa (NIA), da Hukumar DSS, da kula da Gandun Daji, da Rundunar ‘Yansandan da kuma Sojojin Nijeriya. Shirin na daga cikin Presidential Forest Guards Initiative, wanda ke da nufin ƙwato dazukan da ‘yan ta’adda, da ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane ke amfani da su a matsayin mafaka, inda ake sa ran masu gadin dajin za su yi aiki tare da hukumomin tsaro wajen tattara bayanan sirri da sintiri a yankunan dazuka.

Kaduna
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    TCN Ta Kammala Gyaran Layin Wutar Lantarkin Zaria–Funtua 132kV
  • Abubakar Sulaiman
    DSS Ta Kama ‘Yar Jarida Zainab Sodiq Kan Zargin Mallakar Drone Ba Tare da Cikakkun Takardu ba
  • Abubakar Sulaiman
    Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata
  • Abubakar Sulaiman
    Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi
Tsaro

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

June 19, 2026

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Auto Draft

TCN Ta Kammala Gyaran Layin Wutar Lantarkin Zaria–Funtua 132kV

July 9, 2026
Auto Draft

DSS Ta Kama ‘Yar Jarida Zainab Sodiq Kan Zargin Mallakar Drone Ba Tare da Cikakkun Takardu ba

July 9, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

July 9, 2026
Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

July 9, 2026
’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A  Jihar Benuwai

’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A Jihar Benuwai

July 9, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

July 9, 2026
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.