ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

“Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

by Abubakar Abba
40 minutes ago
Kaduna

Mata mabiya addinin Kirista da ƴan’uwansu Musulmai, sun ce mutunta ƴancin addinai ita ce hanya ɗaya tilo da za a iya wanzar da zaman lafiya a Jihar Kaduna.

Sun bayyana haka ne a cikin wata sanarwar sakamakon taro da Cibiyar Sulhu Tsakanin Addinai (IMC) da ke da shalkwata a Kaduna ta shirya masu tare da tallafin ofishin jakadanci na ƙasar Jamus da ke Abuja.

Kazakila, sun bayyana cewa za a iya wanzar da zaman lafiya ne a cikin al’umominsu idan aka ƙarfafa masu giwa.

ADVERTISEMENT

Taken taron shi ne, ƙarfafa wa mata giwa domin wanzar da shugabaci, kare ƴancin Ɗan’adma da kuma ƙara ƙarfafa mulkin dimokiraɗiyya a Kaduna.

Sun sanar da cewa idan mata suka samu damar riƙe madafun iko, hakan zai ba su damar wanzar da shirye-shiyen da gudanar da ayyukan da suka shafi wanzar da zaman lafiya, a cikin al’umma.

LABARAI MASU NASABA

NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

Haka kuma sun jaddada muhimmancin ba su horo kan yadda za su wanzar da yin sulhu a duk lokacin da aka samu aukuwar wani rikici a cikin al’umma, inda kuma suka nuna kyama kan furta kalaman haddasa ƙiyayya da tunzura jama’a a tsakanin mabiya addinai.

Sun sanar da cewa akwai buƙatar a samar da shirye-shiyen koyon sana’o’in hannu a tsakanin matan da ke a jihar, domin su zama masu dogaro da kansu tare da yin magana da murya ɗaya kan lamuran da suka shafi harkokin mata.

Matan sun kuma sanar da yin aiki da koyarwar da ke a cikin litattafan Bibul da Alƙur’ani, wanda zai taimaka masu wajen kasancewa jakadun wanzar da zaman lafiya a cikin al’ummarsu.

Taron ya kuma buƙaci gwamnatin Kaduna da ta samar da tsare-tsare da shirye-shiryen tare da samar da wadatattun kuɗaɗe na wanzar da zaman lafiya, musamman ta hanyar gudanar da yin gangamin wanzar da zaman lafiya a jihar.

Sun kuma buƙaci hukumomin tsaro a jihar da su haɗa ƙarfi da karfe da mata, musamman domin a samu nasarar daƙile duk wata barazana ta rashin hankali da ka iya kunno kai a jihar.

Sun yi kira ga kafafen yaɗa labarai da su ƙirƙiro da shiye-shiryen wanzar da zaman lafiya a ɗaukacin faɗin jihar, inda kuma suka jinji wa cibiyar bisa shirya masu taron.

Taron ya kuma samu halartar manyan malaman addinin Kirita, Musulmai, ƙungiyoyi masu zaman kansu, shugabannin ƙungiyoyin matasa da abokan haɗaka.

Kaduna
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Ɗaura Ɗamarar Magance Matsalolin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Matatar Ɗangote Ta Ƙaryata Iƙirarin Dillalan Man Fetur 

MASU ALAKA

NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN
Labarai

NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

July 10, 2026
Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
Labarai

Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Labarai

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

July 10, 2026
Next Post
NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma'aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

LABARAI MASU NASABA

NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

“Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

July 10, 2026
Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

July 10, 2026
Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu

Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu

July 10, 2026
Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisar Kan Gyaran Kudirin Dokar Shari’ar Manyan Laifuka

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisar Kan Gyaran Kudirin Dokar Shari’ar Manyan Laifuka

July 10, 2026
Taƙaddamar Kafa Hukumar Bogi: Tinubu Ya Umarci A Yi Binciken Ƙwaƙwaf

Taƙaddamar Kafa Hukumar Bogi: Tinubu Ya Umarci A Yi Binciken Ƙwaƙwaf

July 10, 2026
Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

July 10, 2026
Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin

Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin

July 9, 2026
Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni

Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni

July 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.