Mata mabiya addinin Kirista da ƴan’uwansu Musulmai, sun ce mutunta ƴancin addinai ita ce hanya ɗaya tilo da za a iya wanzar da zaman lafiya a Jihar Kaduna.
Sun bayyana haka ne a cikin wata sanarwar sakamakon taro da Cibiyar Sulhu Tsakanin Addinai (IMC) da ke da shalkwata a Kaduna ta shirya masu tare da tallafin ofishin jakadanci na ƙasar Jamus da ke Abuja.
Kazakila, sun bayyana cewa za a iya wanzar da zaman lafiya ne a cikin al’umominsu idan aka ƙarfafa masu giwa.
Taken taron shi ne, ƙarfafa wa mata giwa domin wanzar da shugabaci, kare ƴancin Ɗan’adma da kuma ƙara ƙarfafa mulkin dimokiraɗiyya a Kaduna.
Sun sanar da cewa idan mata suka samu damar riƙe madafun iko, hakan zai ba su damar wanzar da shirye-shiyen da gudanar da ayyukan da suka shafi wanzar da zaman lafiya, a cikin al’umma.
Haka kuma sun jaddada muhimmancin ba su horo kan yadda za su wanzar da yin sulhu a duk lokacin da aka samu aukuwar wani rikici a cikin al’umma, inda kuma suka nuna kyama kan furta kalaman haddasa ƙiyayya da tunzura jama’a a tsakanin mabiya addinai.
Sun sanar da cewa akwai buƙatar a samar da shirye-shiyen koyon sana’o’in hannu a tsakanin matan da ke a jihar, domin su zama masu dogaro da kansu tare da yin magana da murya ɗaya kan lamuran da suka shafi harkokin mata.
Matan sun kuma sanar da yin aiki da koyarwar da ke a cikin litattafan Bibul da Alƙur’ani, wanda zai taimaka masu wajen kasancewa jakadun wanzar da zaman lafiya a cikin al’ummarsu.
Taron ya kuma buƙaci gwamnatin Kaduna da ta samar da tsare-tsare da shirye-shiryen tare da samar da wadatattun kuɗaɗe na wanzar da zaman lafiya, musamman ta hanyar gudanar da yin gangamin wanzar da zaman lafiya a jihar.
Sun kuma buƙaci hukumomin tsaro a jihar da su haɗa ƙarfi da karfe da mata, musamman domin a samu nasarar daƙile duk wata barazana ta rashin hankali da ka iya kunno kai a jihar.
Sun yi kira ga kafafen yaɗa labarai da su ƙirƙiro da shiye-shiryen wanzar da zaman lafiya a ɗaukacin faɗin jihar, inda kuma suka jinji wa cibiyar bisa shirya masu taron.
Taron ya kuma samu halartar manyan malaman addinin Kirita, Musulmai, ƙungiyoyi masu zaman kansu, shugabannin ƙungiyoyin matasa da abokan haɗaka.














