ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

by Abubakar Sulaiman
1 minute ago
Khomeini

A ranar Asabar ce aka fara hidimar jana’izar tsohon jagoran addinin Iran, Ayatollah Ali Khamenei, wanda ya jagoranci ƙasar na tsawon shekara 36.

An kashe shi a wasu hare-haren Amurka da Isra’ila a ƙarshen watan Fabrairun 2026.

Wannan na zuwa ne shekara 37 bayan jana’izar jagoran addinin ƙasar na farko, Ruhullah Khomeini da aka gudanar a birnin Tehran.

ADVERTISEMENT

Bayan rasuwarsa ne majalisar ƙwararrun ƙasar suka zaɓi Ali Khamenei a matsayin sabon jagodan addinin ƙasar.

Jana’izar Ruhollah na ɗaya daga cikin manyan tarukan jana’izar da aka samu yamutsi a tarihi.

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

A cewar jami’an Iran, fiye da mutum miliyan 10 ne suka halarci taron jana’izar, lamarin da ya sa Kundin Adana Tarihi na Guinness ya ayyana taron jana’izar a matsayin wadda ba a taɓa ganin irinta ba a tarihin duniya, idan aka kwakwanta yawan waɗanda suka halarta da yawan al’ummar ƙasar.

Duk da cewa an samu labarin tsananta jikinsa gabanin rasuwar tasa, labarin mutuwar tasa ta girgiza ƴan ƙasar da magoya bayansa da dama.

Ya rasu shekara 10 bayan juyin-juya halin ƙasar da ya kifar da gwamnatin tsohon sarkin ƙasar da ake kira Sha, tare da kafa sabon tsaron gwamnatin Jamhuriyar Musulunci, kuma ƙasa da shekara ɗaya bayan kammala yaƙin Iran da Iraƙi.

Me ya faru a wajen “bankwana” da binne gawar?

A cikin wani rahoto na musamman mai suna “Ruhollah”, da aka naɗa kan rayuwar Ayatullah Khamne’i, ya nuna hotunansa a kwanakin ƙarshe na rayuwarsa a asibiti a kashi na ƙarshe na shirin.

A cikin rotunan, an ga Khomeini na kwance a kan gadon asibiti, likitoci da ƴan’uwansa na kewaye da shi.

An ga yadda jikinsa ya yi la’asar, yana motsi cikin tsananin wahalar jinya da kuma ba ya iya magana.

Rahoton na musamman ya kuma nuna wasu lokutan da Ruhollah Khomeini ke addu’a tare da taimakon wasu mutane, a wasu wuraren kuma an ga wasu mutanen da ke kusa da shi na ƙoƙarin ciyar da shi.

Sannan an ga hotunan likitoci da makusantansa na ƙoƙarin tallafo sh.

An ƙarƙare rahoton da nuna hotunan wasu ƴan’uwansa na kuka da jimami bayan samun labarin rasuwarsa.

Ruhollah Khomeini ya rasu ne da maraicen 3 ga watan Yunin 1989, yayin da gidajen radiyo da talbijin na ƙasar suka sanar da labarin washe gari da safe.

A lokacin hukumomin ƙasar sun ayyana makokin kwana 40, kuma magoya bayansa sun nuna jimami a kan titinan ƙasar.

A lokacin da labarin rasuwarsa ya yaɗu, dandazon mutane daga sassan ƙasar daban-daban sun ɗunguma zuwa birnin Tehran domin halartar jana’izar.

A ranar 5 ga watan Yuni ne aka kai gawarsa zuwa babban masallacin Juma’a ana birnin Tehran, domin bankwana da ita.

Bayan shirya gawar cikin likkafani, an sanya ta cikin gilashi mai haske ta yadda mutane za su iya hango ta, aka kuma ɗora ta kan wani abu mai tudu ta yadda duk wanda ya shiga masallacin zai hango ta.

Hotunan da aka ɗauka ta kyamarorin da ke yawo a sama sun nuna yadda dandazon mutane suka yi wa masallacin dafifi.

Wasu na kuka wasu na bugun ƙirgi wasu na jimami, duk a cikin alhinin mutuwar tsohon jagoran addinin.

An samu labarin cewa mutane da dama ne suka suma sakamakon zafi da cunkoson jama’a a wurin taron.

Gawar ta kwana a masallacin har zuwa washe gari, inda aka ɗauke ta zuwa maƙabartar Behesht Zahra da ke kudancin birnin Tehran, domin binne ta.

A nan ne kuma dandazon mutane suka sake taruwa, lamarin da ya ci ƙarfin jami’an tsaron da ke bayar da kariya a wurin.

An tsara tafiya daga tsakiyar Tehran zuwa Behesht Zahra, kusan kilomita 30 tsakani.

Hotunan da aka ɗauka sun nuna yadda mutane suka yi dafifi a kan titin Tehran zuwa Behesht Zahra.

Motar da ta ɗauki gawarsa ta riƙa tafiya a hankali saboda cunkoson jama’a a kan titin.

Waɗanda suka shirya jana’izar sun gaza aiwatar da tsarin jana’izar kamar yadda suka shirya tun da farko saboda yawan jama’a.

Jami’an tsaro da dakarun juyin juya halin ƙasar, sun shiga domin buɗe hanya, don samar wa motar da ke ɗauke da gawar hanya.

Yayin da ake haka a kan hanya, can kuwa a garin na Behesht Zahra tuni ya cika maƙil da jama’a, wani abu da ya haifar da wahala wajen shigar da gawar zuwa maƙabartar.

Daga ƙarshe bayan da aka fahimci babu wurin da gawar za ta shiga garin ta ƙasa, hukumomi sun sake shiri, inda suka yanke shawarar ɗaukar gawar a jirgi mai saukar ungulu zuwa cikin maƙabartar kai-tsaye.

To amma duk da haka, can ma a maƙabartar mutane sun cika ta maƙil.

Yayin da jirgin ya sauka a maƙabartar, dubban mutane sun ruga da gudu domin samun damar taɓa gawar da nufin samun tabarruki.

Hotunan da aka ɗauka sun nuna yadda mutane suka tunkari jirgin da nufin taɓa gawar idan an fito da ita, lamarin da ya haifar da turmutsutsu a maƙabartar.

Jami’an tsaro da dakarun juyin juya hali sun samu nasarar ƙwace iko da gawar, tare da maida ta jirgin, inda ya sake tashi sama.

Akbar Hashemi Rafsanjani, wanda shi ne kakakin majalisar dokokin ƙasar na lokacin, ya halarci wurin a cikin jirgi mai saukar ungulu, inda ya sanya idanu a lokacin da ake maido da doka da oda a maƙabartar.

Ahmad Khomeini, ɗa ga Ruhollah Khomeini, shi ma ya halarci jana’izar.

A daidai lokacin ne kuma gidan radion ƙasar, ya sanar da ɗage jana’izar domin bai wa dandazon mutane damar ficewa daga maƙabartar.

Bayan wani lokaci, jirgin da ke ɗauke da gawar ya samu damar sauka a inda ya dace, inda kuma aka samu nasarar yin jana’izar.

‘Mutum 10,200,000 ne suka halarci jana’izar’

A cewar wasu alƙaluma daga Kundin Adana Tarihi na Guinness dandazo da matsin da aka samu a wajen jana’izar ya haifar da mutuwar mutum takwas da raunata 500.

Majiyar Kundin ta ƙara da cewa adadin mutanen da suka halarci jana’izar ya kai mutum miliyan 10,200,000.

Ayatollah Khomeini, ya kasance ɗaya daga cikin mafiya tasiri a tsarin shugabanci da siyasar da kuma Addini a tarihin Iran.

Shi ne ya jagoranci juyin juya halin da ya kifar da gwamnatin Pahlaɓi.

Ali Khamene’i ya gaje shi a 1989, inda ya zama jagoran addainin ƙasar na biyu, kuma mafi jimawa a mulki, inda ya taka muhimmiyar rawa wajen tsara muradun ƙasar da alaƙarta da ƙasashen waje.

Magoya bayan shagabannin biyu, na kallonsu a matsayin wata alama ta ƴancin kai da turjiya daga ƙasashen Yamma, yayin da masu suka ke zarginsu da tattare duka ikon ƙasar a hannayensu.

Jana’izar Khamene’i

A yanzu haka jami’an Iran na shirya jana’izar Ayatollah Ali Khamenei

Hukumomin Iran sun ce suna sa ran samun miliyoyin mutanen da za su halarci jana’izar Ayatollah Ali Khamenei, wadda aka tsara yi cikin tsaurara matakan tsaro.

Haka kuma, yadda Mista Khamenei ya rasa ransa ya sa jana’izar za ta ɗauki wata alama ta musamman.

A bayanan da suke yi, jami’an gwamnatin Iran da magoya bayansa na bayyana shi a matsayin ”Shahidi”, wata kalma mai ɗauke da tarin daraja a Addinin Musulunci.

Khomeini
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN
  • Abubakar Sulaiman
    Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisar Kan Gyaran Kudirin Dokar Shari’ar Manyan Laifuka
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’
  • Abubakar Sulaiman
    TCN Ta Kammala Gyaran Layin Wutar Lantarkin Zaria–Funtua 132kV

MASU ALAKA

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz
Manyan Labarai

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
Kasashen Ketare

Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

July 5, 2026
Iran Za Ta Rufe Tehran A Mako Mai Zuwa Domin Jana’izar Ayatollah Ali Khamenei
Kasashen Ketare

Iran Za Ta Rufe Tehran A Mako Mai Zuwa Domin Jana’izar Ayatollah Ali Khamenei

July 1, 2026

LABARAI MASU NASABA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

July 10, 2026
NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

“Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

July 10, 2026
Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

July 10, 2026
Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu

Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu

July 10, 2026
Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisar Kan Gyaran Kudirin Dokar Shari’ar Manyan Laifuka

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisar Kan Gyaran Kudirin Dokar Shari’ar Manyan Laifuka

July 10, 2026
Taƙaddamar Kafa Hukumar Bogi: Tinubu Ya Umarci A Yi Binciken Ƙwaƙwaf

Taƙaddamar Kafa Hukumar Bogi: Tinubu Ya Umarci A Yi Binciken Ƙwaƙwaf

July 10, 2026
Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

July 10, 2026
Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin

Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin

July 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.