Hukumar Kula da Shaidar Ɗan Ƙasa (NIMC) ta ƙara ƙarfafa haɗin gwuiwa da manyan ma’aikatun gwamnati domin hanzarta aiwatar da sabuwar Dokar NIMC ta 2026, faɗaɗa rajistar Lambar Shaidar Ɗan Ƙasa (NIN) da kuma bunƙasa amfani da tsarin shaidar dijital a shirye-shiryen gwamnati da ɓangaren kamfanoni masu zaman kansu.
Babbar Daraktar Hukumar NIMC, Abisoye Coker-Odusote, ta gudanar da tarurruka daban-daban a Abuja da Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai na Ƙasa, Mohammed Idris; da Ministan Harkokin Agaji, Dakta Bernard Doro; da Ƙaramin Ministan Masana’antu, Kasuwanci da Zuba Jari, Sanata John Owan Enoh. Tattaunawar ta mayar da hankali ne kan faɗaɗa tsarin shaidar dijital na Nijeriya, ƙarfafa kariyar bayanai, inganta ayyukan gwamnati da kuma ƙara amfani da NIN a dukkan shirye-shiryen gwamnati da masu zaman kansu.
A yayin taron, Mohammed Idris ya yaba wa shugabancin NIMC bisa abin da ya kira gagarumin ci gaba da hukumar ta samu a cikin shekaru uku da suka gabata. Ya bayyana cewa sama da ‘yan Nijeriya miliyan 136 sun riga sun yi rajista a kundin shaidar ɗan ƙasa, amma ya ce har yanzu miliyoyin mutane ba su yi rajista ba. Saboda haka, ya buƙaci NIMC ta ƙara ƙaimi wajen kai rajistar zuwa matakin ƙananan hukumomi ta hanyar haɗin gwiwa da Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa (NOA), wadda ke da ofisoshi a dukkan ƙananan hukumomin ƙasar.
Ministan ya jaddada cewa tsarin shaidar dijital na da matuƙar muhimmanci wajen tsara manufofin ƙasa, aiwatar da gyaran tattalin arziki da tabbatar da kowa ya amfana da shirye-shiryen gwamnati. Ya kuma yabawa NIMC bisa yadda ta kare bayanan da ke cikin kundinta ba tare da rahoton wata matsalar satar bayanai ba, tare da tabbatar da cewa ma’aikatun da ke ƙarƙashin Ma’aikatar Yaɗa Labarai, ciki har da Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) da NOA, za su ci gaba da tallafa wa hukumar wajen wayar da kan jama’a kan muhimmancin yin rajistar NIN.













