Hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) ta fitar da sanarwar gargadi ga masu amfani da ke shirin bin babbar hanyar Abuja zuwa Kaduna sakamakon matsanancin cunkoson ababen hawa da ya biyo bayan karuwar zirga-zirga domin bukukuwan Eid-El-Kabir.
Hukumar ta kuma bayyana cewa ayyukan gyaran hanya da kuma ruwan sama mai yawa na daga cikin abubuwan da ke kawo cikas ga warware cunkoson ababen hawan cikin sauki.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kwamandan sashen Kaduna na FRSC, Kwamanda Andrew Longkam, ya sanya wa hannu kuma aka fitar ranar Lahadi a Kaduna.
Sanarwar ta ce babban wurin da cunkoso ya fi kamari shi ne yankin Nasarawa Azara tsakanin garuruwan Katari da Jere.
Hukumar ta danganta tsanantar cunkoson da rashin hakuri da kuma rashin bin tsarin hanya yadda ya kamata daga wasu masu ababen hawa ke yi.
Ta ce rundunar FRSC reshen Kaduna ta tura karin jami’ai domin kula da zirga-zirga a yankin da abin ya shafa, tare da hadin gwiwar rundunar sojin Nijeriya da sauran masu ruwa da tsaki.















Discussion about this post