Ƙaramin ministan tsaro, Bello Matawalle, ya bayyana cewa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ne zai sake samun nasara a zaɓen 2027, yana mai cewa jam’iyyar APC na ci gaba da samun goyon baya a faɗin ƙasar nan.
Tsohon gwamnan Zamfaran ya bayyana hakan ne ranar Asabar a garinsu yayin wani taron gangamin APC, inda dubban magoya bayan jam’iyyar suka hallara domin nuna goyon baya ga wa’adin mulki na biyu na Tinubu.
A wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Ahmad Dan-Wudil, ya fitar, Matawalle ya ce yawan jama’ar da suka halarci taron alama ce ta yadda ‘yan Nijeriya ke ci gaba da amincewa da APC da shugabancinta.
“Bola Ahmed Tinubu zai sake lashe zaɓe a 2027. APC na da ƙarfin kuma tana da amincewar jama’a,” in ji Bello Matawalle.
Ministan ya ƙara da cewa al’ummar Zamfara na ci gaba da goyon bayan APC tare da kira ga mambobin jam’iyyar da su ƙara haɗa kai da kuma karfafawa gangamin siyasa a matakin ƙasa domin shirye-shiryen babban zaɓen 2027.















Discussion about this post