Kwana huɗu bayan sace ɗimbin masu ibada a wani babban masallaci da ke yankin Dakera, a Karamar Hukumar Borgu ta Jihar Neja, gwamnatin jihar ta ce har yanzu ba ta tabbatar da ainihin adadin mutanen da aka yi garkuwa da su ba.
Rahotanni sun bayyana cewa an yi garkuwa da masu ibada daga al’ummomin Gidan-Zana da Kpenya da ke Dekara, ciki har da dagacin kauyen da babban limamin masallacin, yayin gudanar da sallar Juma’a a ranar Juma’ar da ta gabata.
An ruwaito cewa kimanin masu ibada 200 ne suke cikin masallacin lokacin da ‘yan bindiga suka kai farmakin bayan an kammala sallar, inda suka tilasta musu bin su zuwa cikin daji.Da yake mayar da martani kan lamarin a jiya Lahadi, gwamnatin jihar ta ce har yanzu tana kan tantance adadin mutanen da aka sace da sauran bayanan da suka shafi lamarin.
Kwamishinan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a na jihar, Obed Nuhu Nana, ya ce, “Gwamnati na kira ga jama’a, musamman mazauna al’ummomin da lamarin ya shafa, da su guji yaɗa rahotannin da ba a tabbatar da sahihancinsu ba, adadin waɗanda abin ya shafa ko kuma bayanan da aka yi hasashe a kansu, wadanda ka iya kara jefa jama’a cikin fargaba ko kuma kawo cikas ga kokarin jami’an tsaro da suke yi na ganin an kuɓutar da waɗanda lamarin ya shafa.”
Nana ya bayyana cewa an tura hadin gwiwar jami’an tsaro zuwa yankin da lamarin ya faru domin tantance halin da ake ciki, bin sawun wadanda suka aikata laifin da kuma taimakawa wajen ceto mutanen da aka yi garkuwa da su.
Ya kara da cewa, “Saboda yanayin sirrin aikin da ake gudanarwa a halin yanzu, ba za a bayyana cikakkun bayanai kan zirga-zirga da yadda aka jibge jami’an tsaro ba a wannan lokaci.”














