Kasar Sin ta ce, daukaka manufofi da ka’idojin yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya, ta dace da muradun dukkan kasashe. Jakadan Sin kan harkokin kwance damarar makamai Shen Jian ne ya bayyana haka a ranar Juma’a, yayin taron nazarin yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya na 11, inda ya ce, Sin tana takaicin yadda taron ya gaza cimma matsaya kan kwararan matakai.
Ya ce, cikin makonni 4 da suka gabata, dukkan bangarori sun yi musayar ra’ayi mai zurfi kan yanayin da tsaro ke ciki a duniya, sun kuma yi bitar tsarin aiwatar da yarjejeniyar da kuma kokarin lalubo matakan inganta burin hana yaduwar makaman nukiliya da kawar da su da amfani da makamashin nukiliya ta hanyar lumana.
Ya ce, duk da sabanin da aka samu kan batutuwa da dama, dukkan bangarorin na burin daukakawa da karfafa karfi da ingancin yarjejeniyar da kuma samun tsaro na bai daya.Ya ce, Sin na kira ga dukkan kasashe masu ruwa da tsaki su rungumi tsarin cudanyar bangarori daban daban da neman tsaro na bai daya da kokarin kyautata muhallin tsaron kasa da kasa da yankuna da kawar da tushen matsalolin yaduwar makaman nukiliya da samar da muhalli mai dacewa na samun nasarorin kawar da makaman da fadada hadin gwiwar kasa da kasa kan amfani da makamashin nukiliya ta hanyar lumana. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post