Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya sanar da cewa gwamnatin jihar za ta sayar wa manoma taki a farashi mai rangwame na Naira 32,000 kacal kan kowanne buhu mai nauyin kilo 50 domin noman daminar shekarar 2026.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Talata yayin ƙaddamar da sayarwa da rarraba takin a birnin Gombe, inda ya ce matakin na daga cikin dabarun gwamnatin jihar na tabbatar da wadatar abinci da kuma rage wa manoma nauyin tsadar kayan noma.
Ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta sayo tan 12,000 na takin NPK 20:10:10, wanda ya yi daidai da buhu 240,000, a farashin Naira 64,000 kan kowanne buhu.
Sai dai ya ce gwamnatin ta yanke shawarar rage farashin da kashi 50 cikin 100 domin tallafa wa manoma.
Matakin ya samu karɓuwa daga manoma da masu ruwa da tsaki a fannin noma, waɗanda suka bayyana cewa rangwamen zai taimaka wajen ƙara yawan noma da rage matsin kuɗaɗen da ake kashewa wajen samar da amfanin gona.















Discussion about this post