Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), ta sanar da kammala jigilar dawowar sama da alhazan Nijeriya 38,000 daga Ƙasar Saudiyya bayan gudanar da aikin Hajjin shekarar 2026.A wata sanarwa da kakakin hukumar, Fatimah Usara, ta fitar, ta ce jirgi na ƙarshe da ke ɗauke da alhazan Jihar Zamfara ana sa ran zai sauka a Nijeriya a ranar Talata.
Usara ta bayyana cewa kammala jigilar dawowar alhazan ya nuna ƙarshen dukkan ayyukan Hajjin 2026, wanda ya haɗa da jigilar alhazan Nijeriya zuwa da kuma dawowarsu daga Saudiyya cikin nasara.
Ta ce wannan babban aiki ne na ƙasa wanda ya gudana cikin tsari, tare da haɗin gwiwar hukumomi da masu ruwa da tsaki daban-daban.
Sai dai ta bayyana cewa har yanzu akwai alhazan Nijeriya 12 da ke ci gaba da karɓar magani a asibitoci daban-daban a Saudiyya sakamakon wasu matsalolin rashin lafiya.
Hukumar ta ce tana sa ido kan lafiyar waɗannan alhazai tare da tabbatar da cewa suna samun kulawar da ta dace har zuwa lokacin da za su samu sauƙi kuma a dawo da su gida lafiya.















Discussion about this post