Da safiyar yau Talata ne firaministan kasar Sin Li Qiang, ya gana da firaministan kasar Guinea Amadou Oury Bah a birnin Dalian. Jami’an biyu sun gana ne yayin da Amadou Oury Bah ke ci gaba da ziyara a Sin don halartar taron dandalin tattalin arziki na duniya na bazara ko DAVOS a takaice.
Li Qiang ya bayyana cewa, Guinea ita ce kasa ta farko dake kudu da hamadar Sahara da ta kulla alakar diflomasiyya da jamhuriyyar jama’ar kasar Sin. Ko da yake kasashen biyu suna da nisa da juna, amma suna da dakon zumunci na tsawon lokaci.
Li Qiang ya kuma nuna cewa, bangaren Sin yana son karfafa hada shirin raya tattalin arziki da zamantakewar al’umma na shekaru biyar-biyar karo na 15 na Sin, da dabarun “Simandou 2040” na Guinea, tare da yin amfani da manufofin sokewa kasashen Afirka gaban dayan haraji da Sin ta aiwatar, da kuma inganta hanyar samar da saukin shigo da kayayyakin noma na kasashen Afirka zuwa Sin, don inganta matakin hadin gwiwa a fannoni kamar na kasuwanci, da noma, da ma’adanai da kuma cimma babban matakin hadin gwiwa mai amfani ga juna.
A nasa bangare, Amadou Oury Bah ya bayyana cewa, nasarorin da Sin ta samu a ci gaban tattalin arziki sun ja hankalin duniya, kuma sun zama abin koyi ga kasashe masu tasowa. Bangaren Guinea yana godewa taimakon da bangaren Sin ya dade yana bayarwa ga ci gaban tattalin arziki da zamantakewar Guinea, kuma yana fatan kara hadin gwiwa da bangaren Sin, don aiwatar da muhimman yarjejeniyoyin shugabannin kasashen biyu, ta yadda za su zurfafa manyan ayyuka kamar Simandou, da fadada hadin gwiwa a fannoni kamar na kasuwanci, da ababen more rayuwa, da noma, da makamashi, da fasaha da kuma inganta matakin hadin gwiwar masana’antu tsakaninsu. (Amina Xu)















Discussion about this post