Wani kamfanin gine-gine na kasar Sin ya kammala wani babban aikin samar da ruwan sha a garin Karu, garin da ke samun saurin bunkasa da ke raɓe da babban birnin tarayyar Nijeriya Abuja, inda hakan ya samar da tsaftataccen ruwa ga dubban mazauna garin.
Shugaban Nijeriya Bola Tinubu wanda mataimakinsa Kashim Shettima ya wakilta ne ya kaddamar da aikin samar da ruwan a jiya Litinin a garin na Karu, wanda kamfanin ayyukan injiniya na kasar Sin na CGC Nigeria Limited ya kammala cikin watanni 10.
Aikin ya kunshi jawo ruwa daga tafkin da ake da shi kuma ya kunshi sanya bututu na tsawon sama da kilomita 194, tare da hade layukan rarraba ruwan sama da 1,000 ga sassan unguwannin garin. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post