Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun, ya ce murabus din firaministan Birtaniya Keir Starmer, lamari ne na cikin gida na Birtaniya, kuma Sin ba za ta yi tsokaci game da hakan ba. Ya kuma bayyana cewa ya kamata Sin da Birtaniya su yi aiki tare domin zurfafa hadin gwiwar bangarorin biyu da kuma karfafa mu’amala tsakanin bangarori daban-daban.Guo ya bayyana haka ne a gun taron manema labarai na yau da kullum da aka gudanar yau Talata.
Dangane da bikin baje kolin tsarin hada-hadar samar da kayayyaki na kasa da kasa na Sin ko CISCE a takaice karo na hudu da ake gudanarwa a birnin Beijing, Guo ya ce taron na wannan karo ya jawo hankalin masu baje koli fiye da 1200 daga kasashe, da yankuna, da ma kungiyoyin duniya guda 85, inda adadin masu baje kolin na kasashen waje ya kai fiye da kaso 36%.
Guo ya kara da cewa, sha’awar shiga baje kolin na kamfanoni daga kasashe daban-daban na nuna yadda suke mai da hankali kan babbar kasuwar Sin, da kuma amincewarsu da makomar tattalin arzikin kasar.(Safiyah Ma)














Discussion about this post