Rundunar ’Yansandan Jihar Adamawa ta sanar da kama wasu mutane 57 da ake zargi da kasancewa cikin wata ƙungiyar masu aikata laifuka da ta addabi birnin Yola da wasu ƙananan hukumomin jihar.
Mai magana da yawun rundunar, Suleiman Nguroje, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Talata.
A cewarsa, kamen na daga cikin ci gaba da ƙoƙarin rundunar na kawar da masu aikata laifuka daga al’umma tare da ƙarfafa tsaron jama’a a faɗin jihar.
Ya ce: “A ci gaba da ƙoƙarin rundunar na tsaftace al’umma daga masu aikata laifuka da kuma tabbatar da tsaron jama’a, an gudanar da wani samame na haɗin gwiwa a wuraren da aka gano masu aikata laifuka ke ɓuya da kuma wuraren da ake zargin ana aikata laifuka a cikin Jimeta da birnin Yola.”
Rundunar ta bayyana cewa an kai samamen ne a wuraren da aka daɗe ana zargin suna zama mafaka ga masu aikata laifuka, kuma an kama waɗanda ake zargin domin ci gaba da bincike.
Rundunar ta jaddada aniyarta ta ci gaba da gudanar da irin waɗannan ayyuka domin tabbatar da zaman lafiya da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a Jihar Adamawa.














Discussion about this post