Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kashe manoma shida a ranar Litinin a garin Kujijiro da ke Gundumar Kuyello, Ƙaramar Hukumar Birnin Gwari ta Jihar Kaduna, lamarin da ya sake tayar da hankula kan matsalar rashin tsaro a yankin.
Rahotanni sun nuna cewa an kai wa manoman harin ne yayin da suke gudanar da ayyukansu na noma a gonakansu.
Ƙungiyar Birnin Gwari Emirate Progressives Union (BEPU) ce ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta bayyana harin a matsayin abin takaici da matuƙar damuwa.
A cikin wata sanarwa da shugaban ƙungiyar, Isah Muhammad, ya sanya wa hannu, wacce jaridar Daily Trust ta samu, ƙungiyar ta nuna alhini da jimami kan kisan tare da yin Allah-wadai da harin.
BEPU ta ce wannan sabon hari ya sake jefa al’ummomin Birnin Gwari cikin baƙin ciki da fargaba, tana mai lura da cewa Gundumar Kuyello da sauran yankunan gabashin masarautar na ci gaba da fuskantar hare-hare duk da ƙoƙarin da ake yi na dawo da zaman lafiya a yankunan.
Don haka, ƙungiyar tayi kira ga jami’an tsaro da gwamnati da su ƙara ɗaukar matakan gaggawa domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma, musamman a yankunan karkara da ke fama da hare-haren ’yan bindiga.
Lamarin ya ƙara nuna irin ƙalubalen tsaro da manoma ke fuskanta a wasu sassan Arewa maso Yammacin Nijeriya, musamman a lokacin damina da ake gudanar da ayyukan noma.














Discussion about this post