Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya gana da babban sakataren majalisar tsaron kasar Masar Youssef Alaa El-Deen, jiya Litinin a birnin New Delhi na kasar Indiya.
Yayin zantawarsu, Wang wanda memba ne a ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, kana darakta a ofishin hukumar koli ta harkokin wajen kasar Sin, ya ce a bana ake bikin cika shekaru 70 da kafa dangantakar diflomasiyya tsakanin Sin da Masar, kuma Sin a shirye take ta yi aiki tare da Masar wajen mayar da wannan gaba, wata dama ta wanzar da musayar kut-da-kut a matsayin koli, da kyautata amincin siyasa, da daga matsayin hadin gwiwa na hakika, da karfafa tsare-tsaren cudanyar mabambantan sassa a duniya, da ci gaba da inganta cikakken kawance bisa manyan tsare-tsare tsakanin sassan biyu.
Kazalika, a dai jiyan, Wang Yi ya zanta da minista a fadar gwamnatin Afirka ta kudu Khumbudzo Ntshavheni a birnin New Delhi.
Inda ya ce salon kafa rukuni na kebabbun kasashe, da danniya na illata halastattun hakkoki, da muradun dukkanin kasashen duniya, tare da haifar da koma baya ga ka’idojin jagorancin cudanyar sassa kasa da kasa. Ya ce a matsayinsu na kashin bayan jagorancin cudanyar kasashe masu tasowa, kamata ya yi kasashe membobin kungiyar BRICS, su karfafa goyon bayan juna da tsare-tsare, su yi hadin gwiwar mayar da BRICS muhimmiyar alama ta hadin kai da dogaro da kai tsakanin kasashe masu tasowa. Kana su yi aiki tare wajen kare gaskiya da adalci, da wanzar da zaman lafiya da daidaito a duniya. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post