An tabbatar da mutuwar mutum hudu, yayin da wasu da dama suka jikkata, sannan daruruwan iyalai suka rasa matsugunansu sakamakon wata mummunar guguwar iska tare da ruwan sama mai ƙarfi da ya afkawa al’ummomi da dama a Ƙaramar Hukumar Kware ta Jihar Sokoto a ranar Asabar.
Daily Trust ta bayyana cewa, Guguwar ta kuma lalata gidaje da dama tare da yin ɓarna ga muhimman cibiyoyin gwamnati, ciki har da makarantar firamare da wani asibiti.
Biyo bayan lamarin, Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), reshen jihar Sokoto, ta gudanar da bincike a yankunan da abin ya shafa domin tantance irin ɓarnar da aka yi da kuma gano buƙatun gaggawa na waɗanda abin ya shafa.
Yankunan da aka kai ziyara sun haɗa da Mallamawa, Mai Mushe, Kaura, Sabon Gari, Rungin Tsamiya da sauran ƙauyukan da guguwar ta shafa.
Rahoton farko na NEMA ya nuna cewa daruruwan iyalai sun rasa muhallansu bayan gidajensu sun rushe ko kuma sun lalace matuƙa. Haka kuma, mutane da dama sun samu raunuka daban-daban, yayin da aka tabbatar da mutuwar mutum hudu sakamakon wannan iftila’in.














