ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna El-Rufai Ya Rantsar Da Sarkin Jere Na 11

An Nada El-Rufai Sarkin Yakin Jere

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
Yayin rantsar da sabon Sarkin Jere na 11, Mai Martaba Alhaji Abdullahi Daniya

Yayin rantsar da sabon Sarkin Jere na 11, Mai Martaba Alhaji Abdullahi Daniya

A yau Juma’a ne Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmed El-Rufa’i ya rantsar da sabon Sarkin Jere na 11, Alhaji Abdullahi Daniya a wani gagarumin bikin da aka gudanar a babban filin ƙwallon ƙafa na garin Jere.

Bikin wanda ya gudana cikin tsattsauran tsaro, ya samu halartar mataimakiyar gwamnan, Hajiya Hadiza Balarabe da kusan ɗaukacin ‘yan majalisar zartaswa na Jihar Kaduna, da mai martaba Sarkin Zazzau, Alhaji Ahmed Nuhu Bamalli, da Jakadan Nijeriya a Ƙasar Benin, Janar Yusuf Tukur Buratai mai ritaya da Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa, Isah Jere Idris da sauran manyan baƙi daga ko ina a sassan ƙasar nan.

El-Rufai
Gwamna El-Rufai yana gaisuwa ga sabon Sarkin bayan an nada shi Sarkin Yakin Jere

Da yake jawabi bayan rantsarwar, Gwamna El-Rufai ya jaddada muhimmancin zaman lafiya a tsakanin al’umma wanda ya ce shi ne babban ginshiƙin kawo ci gaba mai ma’ana. Ya yaba wa al’ummar Jere bisa yadda suka rungumi zaman lafiya tare da yin jaje ga waɗanda ɓarnar ‘yan bindiga ta shafa.

ADVERTISEMENT

Ya ƙara da cewa, gwamnati na ci gaba da yin duk abin da za ta iya wajen tabbatar da tsaro a faɗin Jihar Kaduna, kana ya nemi a ƙara bai wa jami’an tsaro haɗin kai domin su ji daɗin ɗorewa da ƙwazon da suke nunawa a yanzu haka wajen fatattakar ‘yan ta’addar.

El-Rufai
Hoto na gabadaya tare da manyan bakin da suka halarci bikin

Wakazalika, Gwamna El-Rufai ya yi tsokaci a kan matakan da gwamnatinsa take ci gaba da ɗaukawa wajen kare martabar sarakuna da ɗaga darajojinsu a Jihar Kaduna, inda ya yi nuna da cewa an raba wa Hakimai motoci kuma a yanzu haka gwamnatin na shirin sake raba wasu motoci 88 duk dai ga sarakuna a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

El-Rufai

Ya yi kira ga al’ummar Jere su martaba sabon sarkin nasu da ba shi haɗin kai don ya ji daɗin sauke nauyin da aka ɗora masa na jama’a. Daga nan ya yi addu’ar Allah ya gafarta wa Sarkin Jere na 10, Dakta Sa’ad Usman.

Shi ma da yake jawabi, Shugaban Ƙaramar Hukumar Kagarko, Honarabul Auzara Rabo, ya gode wa Gwamna El-Rufai bisa bisa gagarumin ci gaban da ya kawo yankin ƙaramar hukumar da bai wa matasa dama a dama da su a fagen siyasa wanda ya ce hakan ne ya sa aka samu matashi a karon farko da ke shugabantar ƙaramar hukumar.

A nasa jawabin, mai martaba Sarkin Jere, Alhaji Abdullahi Daniya, ya gode wa dukkan jama’ar da suka halarci bikin, sannan ya jaddada ƙudirinsa na ƙara haɗa kan al’umma da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin masarautar.

  • Fara Raba Muhimman Kayayyakin Zabe Da Kone-konen Ofishoshin INEC: Ga Koshi Ga Kwanan Yunwa

Daga bisani, Sarkin Jere ya naɗa Gwamna El-Rufai sarautar Sarkin Yaƙin Jere tare da miƙa masa malafa, da sandar kiwo da kuma ƙaton bajimin sa domin kiwo.

 

El-Rufai
Abdulrazaq Yahuza
+ postsBio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Next Post
Sin Ta Kakabawa Wasu Amurkawa Biyu Takunkumi

Sin Ta Kakabawa Wasu Amurkawa Biyu Takunkumi

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.