Rundunar ‘Yansandan Nijeriya ta kama Adeniyi Adeyemi, wanda ake zargi tare da kafa hukumar bogi mai suna Presidential Foreign Intervention Promotion Council (PFIPC), a Jihar Osun.
An kama shi ne sa’o’i kaɗan bayan Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta bayar da sammacin kama shi bisa zargin yin jabun takardu, damfara da kuma yin ƙarya da sunan wani.
Mai shari’a Muhammed Umar ya bayar da sammacin ne, bayan Adeyemi ya kasa halartar zaman kotu domin amsa tuhume-tuhumen da ake masa duk da cewa an ɗage shari’ar domin ba shi dama.
Masu gabatar da ƙara sun ce Adeyemi na fuskantar tuhume-tuhume guda takwas, kuma rashin halartar kotun da yake yi akai-akai ya jinkirta fara shari’ar.
Har yanzu rundunar ‘yansanda ba ta fitar da ƙarin bayani kan yadda aka kama shi ba.
Ana sa ran za a gurfanar da Adeyemi a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja domin ci gaba da shari’arsa.













