ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Halarci Taron Farko Na Liyafar Ƙungiyar ‘Yan Jaridun Fadar Shugaban Ƙasa

by Sulaiman
2 days ago

Gwamnan Jihar Zamfara, Dakta Dauda Lawal, ya halarci taron cin abincin dare na farko da Ƙungiyar ‘Yan Jaridun Fadar Shugaban Ƙasa ta shirya, wanda aka gudanar a daren Alhamis a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.

A yayin taron, Gwamna Dauda Lawal ya samu damar sanya wa Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, lambar girmamawa ta Babban Majiɓincin Ƙungiyar ‘Yan Jaridun Fadar Shugaban Ƙasa, wato Grand Patron of the State House Press Corps.

An shirya taron ne domin ƙarfafa alaƙa tsakanin ‘yan jarida da manyan jami’an gwamnati, karrama waɗanda suka yi fice wajen bayar da rahotannin da suka shafi Shugaban Ƙasa, tare da samar da wata dama ta tattaunawa tsakanin kafafen yaɗa labarai da manyan shugabannin gwamnati cikin yanayi na sada zumunci.

ADVERTISEMENT

Da yake jawabi a wajen taron, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya buƙaci ‘yan jarida su ci gaba da riƙon ƙwarewa, gaskiya, da ɗaukar nauyin abin da suke wallafawa.

Ya bayyana kafafen yaɗa labarai a matsayin muhimmin abokan hulɗa wajen gina ƙasa da ƙarfafa dimokuraɗiyya.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Messi Da Mbappé Na Jagorantar Cin Ƙwallaye A Gasar Kofin Duniya

Shugaban ya kuma sake jaddada aniyar gwamnatinsa ta kare ‘yancin aikin jarida da kuma ‘yancin faɗar albarkacin baki kamar yadda Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya ya tanada.

Ƙungiyar ‘Yan Jaridun Fadar Shugaban Ƙasa ta ƙunshi ‘yan jaridar da aka ba izinin yaɗa labaran Shugaban Ƙasa da dukkan ayyukan da ake gudanarwa a cikin Fadar Shugaban Ƙasa.

Taron na farko ya samu halartar Uwargidan Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu; Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume; da Babban Ma’aikacin Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila.

Sauran waɗanda suka halarta sun haɗa da Ministan Kuɗi, Ministan Ilimi, Ministan Lafiya, Ministan Noma, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai na Ƙasa, da kuma Shugabar Ma’aikatan Gwamnatin Tarayya, Didi Esther Walson-Jack.

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo
  • Sulaiman
    Sin Ta Sha Alwashin Karfafa Musaya Da Sweden A Dukkanin Fannoni
  • Sulaiman
    Zulum Ya Bayar Da Cak Na Naira Biliyan 5.81 Domin Biyan Bashin Garatutin Ma’aikata Masu Ritaya
  • Sulaiman
    Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Messi Da Mbappé Na Jagorantar Cin Ƙwallaye A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Messi Da Mbappé Na Jagorantar Cin Ƙwallaye A Gasar Kofin Duniya

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje
Labarai

Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar

July 5, 2026
Next Post
Mutane 600 Ne Kacal Suka Ci Jarabawar Ɗaukar Malaman Firamare Daga Cikin 8,000

Mutane 600 Ne Kacal Suka Ci Jarabawar Ɗaukar Malaman Firamare Daga Cikin 8,000

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

July 5, 2026
Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)

July 5, 2026
Sin Ta Sha Alwashin Karfafa Musaya Da Sweden A Dukkanin Fannoni

Sin Ta Sha Alwashin Karfafa Musaya Da Sweden A Dukkanin Fannoni

July 5, 2026
Messi Da Mbappé Na Jagorantar Cin Ƙwallaye A Gasar Kofin Duniya

Messi Da Mbappé Na Jagorantar Cin Ƙwallaye A Gasar Kofin Duniya

July 5, 2026
Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar

July 5, 2026
Dalilan Da Suka Jawo Aka Ƙi Yin Maraba Da FIM House A Jihar Kano

Dalilan Da Suka Jawo Aka Ƙi Yin Maraba Da FIM House A Jihar Kano

July 5, 2026
Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

July 5, 2026
Zulum Ya Bayar Da Cak Na Naira Biliyan 5.81 Domin Biyan Bashin Garatutin Ma’aikata Masu Ritaya

Zulum Ya Bayar Da Cak Na Naira Biliyan 5.81 Domin Biyan Bashin Garatutin Ma’aikata Masu Ritaya

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.