Shugaban Hukumar Ilimin Bai Ɗaya ta Jihar Nasarawa (NSUBEB), Dakta Kasim Mohammed Kasim, ya bayyana cewa mutum 600 ne kacal suka yi nasarar cin jarabawar ɗaukar sabbin malaman makarantun firamare daga cikin mutum 8,000 da suka rubuta jarabawar.
Ya ce gwamnatin Jihar Nasarawa ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abdullahi Sule ta amince da ɗaukar sabbin malamai 1,000 domin cike guraben koyarwa a makarantun firamare. A cewarsa, mutane 21,000 ne suka nemi aikin, amma bayan tantance takardu mutum 8,000 ne suka cancanci rubuta jarabawar, inda mutum 600 ne kawai suka samu nasara.
Dakta Kasim ya ce abin mamaki ne yadda galibin waɗanda suka faɗi jarabawar malamai ne da ke koyarwa a makarantu masu zaman kansu, duk da cewa tambayoyin jarabawar ba su da wahala. Ya ce, “Idan mutum bai iya cin jarabawar ɗaukar malami ba, ta yaya zai koyar da yara?” Ya kuma jaddada cewa ba zai amince da ɗaukar duk wanda bai ci jarabawar ba, ko da kuwa an turo sunansa ta hannun manyan ‘yan siyasa ko masu faɗa a ji.
Shugaban NSUBEB ya kuma buƙaci al’ummomi su ɗauki makarantun gwamnati a matsayin nasu tare da ba su kariya. Ya ce gwamnatin jihar ta kashe biliyoyin naira wajen gyaran makarantun da suka lalace sakamakon amfani da harabarsu wajen wasan ƙwallon ƙafa, tare da gina sabbin azuzuwa da samar da kujeru da tebura.
Ya bayyana damuwarsa kan yadda wasu ke lalata kadarorin makarantu, yana mai cewa an samu wasu mazauna wani ƙauye a Ƙaramar Hukumar Akwanga sun kwashe tebura da kujeru daga wata makarantar gwamnati. Haka kuma ya ce gwamnati ta haramta amfani da harabar makarantun gwamnati a dukkan ƙananan hukumomi 13 na jihar a matsayin filin horas da ƙwallon ƙafa, tare da gargaɗin masu aikata ɓarnar da su daina ko kuma su fuskanci hukuncin doka.














